Home DUNIYA UAE ta dage haramcin shiga kasarta ga ‘yan Nijeriya

UAE ta dage haramcin shiga kasarta ga ‘yan Nijeriya

Gwamnatin tarayya ta tabbatar da cewa Hadaddiyar Daular Larabawa (UAE) ta dage haramcin shiga ƙasarta da ta yi wa ‘yan Nijeriya.

Wannan na cikin wata sanarwa da gwamnatin ta fitar wacce PRNigeria Hausa ta samu mai dauke da sa hannun Ministan Yada Labarai da Wayar da Kai na Kasa, Mohammed Idris, a ranar Litinin.

Sanarwar ta ce bayan wata tattaunawa da gwamantin Nijeriyar ta yi da ta ƙasar, an sami cim ma matsaya da yarjejeniyar barin ‘yan Nijeriya su ci gaba da shiga kasar ta UAE.

Kazalika, sanarwar ta ce daga yarjejeniyar har da ɗage haramcin bayar da izinin shiga UAE ga dukkan ’yan Nijieriyar dake son shiga kasa

Sanarwar ta ce za a iya fara neman bizar daga 15 ga watan na Yuli, ta kuma bukaci ‘yan kasar su yi nazari kan bizar ta hanyar ziyartar shafinta na intanet domin karin bayani.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp