‘Yan majalisar wakilai sun sadaukar da rabin albashinsu na tsawon wata shida

Ƴan majalisar wakilan Najeriya sun amince da a zabtare kaso 50 na albashinsu na tsawon watanni shida a wani mataki na nuna tausayawa ga yanayin matsin tattalin arziƙi da yunwa da ƴan Najeriya ke ciki a halin yanzu.

Wannan dai ya biyo bayan amincewa da gyaran ga buƙatar da mataimakin shugaban majalisa, Benjamin Kalu ya yi na buƙatar ƴan majalisar da su sadaukar da kaso 50 na albashin nasu na naira 600,000 da suke karɓa.

Hon Benjamin Kalu ya ce zabtare albashin nasu zai taimaka wa gwamnati wajen sauƙaƙa wa ƴan ƙasar rayuwarsu.

Hakan na nufin ƴan majalisar wakilan guda 360 za su tara tsabar kuɗi har naira miliyan 648 wato fiye da rabin naira biliyan ɗaya, idan aka zabtare musu naira miliyan 108 a duk wata.

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya amince da naira 70,000 a matsayin sabon albashi mafi ƙanƙanta ga ma’aikatan gwamnatin ƙasar.

Tinubu ya sanar da sabon albashin ne a ganawarsa da wakilan ƙungiyoyin ƴan ƙwadago na ƙasar a ranar Alhamis.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 33 minutes 57 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 15 minutes 22 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com