Home DUNIYA Gwamnatin Tinubu zata fara bawa dalibai bashin da suka nema

Gwamnatin Tinubu zata fara bawa dalibai bashin da suka nema

Gwamnatin tarayya za ta fara bayar da bashin karatu ga manyan makarantun gwamnatin tarayya kasar da suka nemi bashin nan da mako mai zuwa.

Sai dai shugaban asusun, Akintunde Sawyerr, ya ce ɗaliban makarantun da za su fara sabon zangon karatu ne kawai za su ga kuɗin a asusunsu a yanzu.

A jiya Laraba ne Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya ƙaddamar da asusun mai suna Nigerian Education Loan Fund (Nelfund) a hukumance a fadar shugaban ƙasa da ke Abuja.

Mista Sawyerr ya ce jimillar ɗalibai 170,000 ne suka yi rajista da asusun, waɗanda suka ƙunshi ɗaliban jami’a, da na kwalejojin ilimi da fasaha.

“A taƙaice dai, jimillar ɗalibai 110,000 ne suka nemi bashin. Sun ba da bayanansu tare da miƙa takardun neman, kuma su ne suka cancanta. Amma duk da haka za mu ƙara gudanar da bincike a kansu… Amma da alama sama da mutum 110,000 ne za su fara samun bashin a sati mai zuwa,” in ji shi.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp