Home DUNIYA ‘Yan majalisar wakilai sun sadaukar da rabin albashinsu na tsawon wata shida

‘Yan majalisar wakilai sun sadaukar da rabin albashinsu na tsawon wata shida

Ƴan majalisar wakilan Najeriya sun amince da a zabtare kaso 50 na albashinsu na tsawon watanni shida a wani mataki na nuna tausayawa ga yanayin matsin tattalin arziƙi da yunwa da ƴan Najeriya ke ciki a halin yanzu.

Wannan dai ya biyo bayan amincewa da gyaran ga buƙatar da mataimakin shugaban majalisa, Benjamin Kalu ya yi na buƙatar ƴan majalisar da su sadaukar da kaso 50 na albashin nasu na naira 600,000 da suke karɓa.

Hon Benjamin Kalu ya ce zabtare albashin nasu zai taimaka wa gwamnati wajen sauƙaƙa wa ƴan ƙasar rayuwarsu.

Hakan na nufin ƴan majalisar wakilan guda 360 za su tara tsabar kuɗi har naira miliyan 648 wato fiye da rabin naira biliyan ɗaya, idan aka zabtare musu naira miliyan 108 a duk wata.

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya amince da naira 70,000 a matsayin sabon albashi mafi ƙanƙanta ga ma’aikatan gwamnatin ƙasar.

Tinubu ya sanar da sabon albashin ne a ganawarsa da wakilan ƙungiyoyin ƴan ƙwadago na ƙasar a ranar Alhamis.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp