Home DUNIYA Gwamnan Kano ya kadu bisa rasuwar ‘Yan uwan Kwamishina a jihar

Gwamnan Kano ya kadu bisa rasuwar ‘Yan uwan Kwamishina a jihar

Gwamnan jihar Kano Abba kabir Yusuf ya bayyana kaduwar sa bisa mutuwar ‘yan uwa da ‘yar kwamishinan ma’aikatar ilimi mai zurfi na jihar Dr. Yusuf Ibrahim Kofar Mata. sakamakon iftila’in gobara.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da darakta yada labaran Gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa PRNigeria, wadda ta ambaci gwamnan na nuna damuwa gami da kaduwa bias iftila’in gobarar da ya fada kan ‘yan uwan kamishinan mata guda biyu da kuma ‘yar sa.

Gwamnan Abba ya bayyana gobarar matsayin tashin hankali, wanda ya haddasa masa kaduwa duba da yadda ta kai ga rasa rayukan mutane 3 cikin al’ummar jihar kano, gami da rasa dukiya mai tarin yawa.

Sanarwa ta ce a madadin gwamantin jihar Kano, majalisar zartaswa, da al’ummar jihar Kano suna mika sakon ta’aziyya ga kwamishinan da ‘yan uwa da iyalai, tare da fatan Allah ya karbi shahadar su, ya kuma kiyaye aukuwar hakan anan gaba.

A ranar laraba ne dai Dr. kofara mata ya wallafa wani labara a shafin sa na Facebook, dake cewa gobara ta hallaka masa ‘yan uwan sa mata biyu tare da ‘yar sa guda daya.

A cewar sanarwar, ‘yarsa Maimuna (Islam) da babbar yayarsa Hajiya Khadija da matar dan uwansa Hajiya Juwairiyya sun rasu sakamakon gobarar da ta tashi.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp