Home DUNIYA Gwamnan Kano ya kadu bisa rasuwar ‘Yan uwan Kwamishina a jihar

Gwamnan Kano ya kadu bisa rasuwar ‘Yan uwan Kwamishina a jihar

Gwamnan jihar Kano Abba kabir Yusuf ya bayyana kaduwar sa bisa mutuwar ‘yan uwa da ‘yar kwamishinan ma’aikatar ilimi mai zurfi na jihar Dr. Yusuf Ibrahim Kofar Mata. sakamakon iftila’in gobara.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da darakta yada labaran Gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikowa PRNigeria, wadda ta ambaci gwamnan na nuna damuwa gami da kaduwa bias iftila’in gobarar da ya fada kan ‘yan uwan kamishinan mata guda biyu da kuma ‘yar sa.

Gwamnan Abba ya bayyana gobarar matsayin tashin hankali, wanda ya haddasa masa kaduwa duba da yadda ta kai ga rasa rayukan mutane 3 cikin al’ummar jihar kano, gami da rasa dukiya mai tarin yawa.

Sanarwa ta ce a madadin gwamantin jihar Kano, majalisar zartaswa, da al’ummar jihar Kano suna mika sakon ta’aziyya ga kwamishinan da ‘yan uwa da iyalai, tare da fatan Allah ya karbi shahadar su, ya kuma kiyaye aukuwar hakan anan gaba.

A ranar laraba ne dai Dr. kofara mata ya wallafa wani labara a shafin sa na Facebook, dake cewa gobara ta hallaka masa ‘yan uwan sa mata biyu tare da ‘yar sa guda daya.

A cewar sanarwar, ‘yarsa Maimuna (Islam) da babbar yayarsa Hajiya Khadija da matar dan uwansa Hajiya Juwairiyya sun rasu sakamakon gobarar da ta tashi.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp