Home General Masu garkuwa sun saki mahaifiyar mawaƙi Rarara

Masu garkuwa sun saki mahaifiyar mawaƙi Rarara

Mahaifiyar fitaccen mawaƙin nan na siyasa, Dauda Kahutu Rarara, wato Hajiya Halima Adamu, ta shaƙi iskar ’yanci bayan ’yan bindigar da suka yi garkuwa da ita sun sako ta.

Mawaƙi Rararan ne ya tabbatar da sakin nata a shafinsa na Instagram, inda ya ce an sako ta ne da sanyin safiyar Laraba.

Ya bayyana godiyarsa ga Allah sannan ya gode wa sauran jama’a kan gudunmawar addu’o’in da suka yi mata bayan faruwar lamarin.

Sai dai bai yi bayani kan ko an biya kudin fansa ba kafin sakin nata ko kuma a’a.

A baya dai, rahotanni sun bayyana cewar masu garkuwar sun buƙaci a ba su Naira miliyan 900 kafin su sake ta.

Tun kusan mako uku da suka gabata ne dai wasu ’yan bindiga da ba a san ko su wane ne ba suka sace Hajiya Halima mai kimanin shekaru 75 a gidanta da ke ƙauyen Kahutu a ƙaramar hukumar Ɗanja ta jihar Katsina.

Rarara dai ya yi suna wajen waƙe ’yan siyasa, musamman na jam’iyyar APC mai mulki a Najeriya.

A lokuta da dama, ya sha nuna cewa gwamnatin APCn tana iya kokarinta wajen magance matsalar tsaron da ta addabi ƙasar, ciki har da ta ’yan bindiga da masu garkuwa da mutane.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp