Home General Gwamnan Kano ya mayar da tsohon Sarkin Gaya kan kujerarsa

Gwamnan Kano ya mayar da tsohon Sarkin Gaya kan kujerarsa

Biyo bayan sanya hannu da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi na dokar Samar da masarautu masu daraja ta biyu a jihar Kano. Gwamnan ya amince da nadin Alhaji Muhammad Mahraz Karaye, a matsayin Sarkin Karaye, wanda kafin wannan nadin ya kasance Hakimin karamar hukumar Rogo.

ta cikin wata takardar sanarwa da daraktan yada labaran Gwamnan jihar Sunusi bature Dawakin tofa ya fita, tace nadin ya fara aiki nan take.

Har ila yau, Gwamnan ya amince da nadin Alhaji Muhammad Isa Umar a matsayin Sarkin Rano Mai daraja ta biyu wanda shima kafin nadin ya kasance Hakimi a karamar hukumar Bunkure.

Sai Alhaji Aliyu Ibrahim Abdulkadir Gaya, a matsayin Sarkin Gaya Mai daraja ta biyu wanda dama shine tsohon sarkin Gaya da aka rushe.

A lokacin da yake taya sabbin Sarakunan murna, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya umarce su da su kasance masu kula da al’adu da zaman lafiya da kokari wajen kawo hadin kan al’ummar Masarautun nasu.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp