Home General Gwamnan Kano ya mayar da tsohon Sarkin Gaya kan kujerarsa

Gwamnan Kano ya mayar da tsohon Sarkin Gaya kan kujerarsa

Biyo bayan sanya hannu da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi na dokar Samar da masarautu masu daraja ta biyu a jihar Kano. Gwamnan ya amince da nadin Alhaji Muhammad Mahraz Karaye, a matsayin Sarkin Karaye, wanda kafin wannan nadin ya kasance Hakimin karamar hukumar Rogo.

ta cikin wata takardar sanarwa da daraktan yada labaran Gwamnan jihar Sunusi bature Dawakin tofa ya fita, tace nadin ya fara aiki nan take.

Har ila yau, Gwamnan ya amince da nadin Alhaji Muhammad Isa Umar a matsayin Sarkin Rano Mai daraja ta biyu wanda shima kafin nadin ya kasance Hakimi a karamar hukumar Bunkure.

Sai Alhaji Aliyu Ibrahim Abdulkadir Gaya, a matsayin Sarkin Gaya Mai daraja ta biyu wanda dama shine tsohon sarkin Gaya da aka rushe.

A lokacin da yake taya sabbin Sarakunan murna, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya umarce su da su kasance masu kula da al’adu da zaman lafiya da kokari wajen kawo hadin kan al’ummar Masarautun nasu.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp