Home General Gwamnan Kano ya mayar da tsohon Sarkin Gaya kan kujerarsa

Gwamnan Kano ya mayar da tsohon Sarkin Gaya kan kujerarsa

Biyo bayan sanya hannu da Gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi na dokar Samar da masarautu masu daraja ta biyu a jihar Kano. Gwamnan ya amince da nadin Alhaji Muhammad Mahraz Karaye, a matsayin Sarkin Karaye, wanda kafin wannan nadin ya kasance Hakimin karamar hukumar Rogo.

ta cikin wata takardar sanarwa da daraktan yada labaran Gwamnan jihar Sunusi bature Dawakin tofa ya fita, tace nadin ya fara aiki nan take.

Har ila yau, Gwamnan ya amince da nadin Alhaji Muhammad Isa Umar a matsayin Sarkin Rano Mai daraja ta biyu wanda shima kafin nadin ya kasance Hakimi a karamar hukumar Bunkure.

Sai Alhaji Aliyu Ibrahim Abdulkadir Gaya, a matsayin Sarkin Gaya Mai daraja ta biyu wanda dama shine tsohon sarkin Gaya da aka rushe.

A lokacin da yake taya sabbin Sarakunan murna, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya umarce su da su kasance masu kula da al’adu da zaman lafiya da kokari wajen kawo hadin kan al’ummar Masarautun nasu.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp