Home General Zanga – Zanga babu gudu ba ja da baya a Kano –...

Zanga – Zanga babu gudu ba ja da baya a Kano – WAI

Ƙungiyar kare haƙƙin Ɗan Adam, yaƙi da rashin adalci dama bibiya akan shugabanci na gari wato War Against Injustice (WAI), ta ce babu gudu babu ja da bayan akan Zanga-zangar da ta ayyana gudanarwa daga ranar 1 ga watan Agusta zuwa 10 ga wata.
Babban daraktan ƙungiyar Kwamared Umar Ibrahim Umar ne ya sanar da hakan ta cikin wani saƙon murya da jaridar GTR HAUSA ta samu a yammacin talata, inda ya ce matakin ya zama dole domin nunawa mahukunta halin da talaka yake ciki.
A cewar Kwamared Umar “Ina wannan magana ne a matsayin martani dangane da taron manema labaran da wata ƙungiya tayi a jiya wadda ta ce sun janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa, adan haka mu bamu janye ba kuma zamu gudanar a ranakun da muka ayyana.
Ya ƙara da cewa zasu gudanar da zanga-zangar tasu cikin lumana da kwanciyar hankali kuma ba tare da taɓa haƙƙin al’umma ba, ta yadda zasu nunawa duniya halinda talakawan ƙasar ke ciki na yunwa, fatara da kuma talaucin da yayi musu katutu.
A ƙarshe ƙungiyar tayi fatan Al’ummar jihar zasu basu haɗin kai da goyon baya domin ayi lafiya kuma a kammala lafiya.
A jiya ne ƙungiyar Shugabannin Matasan Arewacin Najeriya ta ce ta janye zanga-zangar da ta shirya gudanarwa, a sakamakon yadda ta gano akwai masu ƙoƙorin rikita ƙasar ta hanyar amfani da zanga-zangar tasu.
PRNigeria hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp