Home General DSS da Hisba sun kama masu safarar mutane a Jihar Kano

DSS da Hisba sun kama masu safarar mutane a Jihar Kano

Hukumar tsaro DSS ta sami nasarar bankado wata kungiyar dake ayyukan fataucin yara kanana a jihar Kano dake Arewa maso Yammacin Nijeriya.

jaridar Solacebase ta ruwaito ofishin cewa Ofishin hukumar na jihar kano ne ya bayyana hakan ranar Talata, inda yace dakarun hukumar sun sami nasarar kama wata mata mai kimanin shekaru 17 da haihuwa tare da kubutar da wata yarinya ýar shekara 4 a duniya daga hannun bata garin wadda ýar asalin Nguru ce a jihar Yobe.

Haka zalika ya kara da cewa Jami’an Hisbah na Jihar Kano sun mika wa wata yarinya ‘yar shekara 4 mai suna A’isha da aka yi garkuwa da ita daga Nguru wadda wata mata ‘yar shekara 17 da aka  sakaya sunanta ta kawo ta Kano bayan sun yi garkuwa da ta.

Hukumar DSS ta bayyana cewa bayan karbar Aisha ‘yar shekara 4 da aka sace tare da wanda ta sace ta, sun gano mutumin da ke safarar kananan yara daga Jihohin Makwafta inda ake sayar da su a Kudancin kasar nan.

“Mun kama babban mai safarar kananan yara daga jihohin makwabta zuwa Kano tare da sayar da su a Kudancin kasar nan.

PRNigeria Hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp