Home General DSS da Hisba sun kama masu safarar mutane a Jihar Kano

DSS da Hisba sun kama masu safarar mutane a Jihar Kano

Hukumar tsaro DSS ta sami nasarar bankado wata kungiyar dake ayyukan fataucin yara kanana a jihar Kano dake Arewa maso Yammacin Nijeriya.

jaridar Solacebase ta ruwaito ofishin cewa Ofishin hukumar na jihar kano ne ya bayyana hakan ranar Talata, inda yace dakarun hukumar sun sami nasarar kama wata mata mai kimanin shekaru 17 da haihuwa tare da kubutar da wata yarinya ýar shekara 4 a duniya daga hannun bata garin wadda ýar asalin Nguru ce a jihar Yobe.

Haka zalika ya kara da cewa Jami’an Hisbah na Jihar Kano sun mika wa wata yarinya ‘yar shekara 4 mai suna A’isha da aka yi garkuwa da ita daga Nguru wadda wata mata ‘yar shekara 17 da aka  sakaya sunanta ta kawo ta Kano bayan sun yi garkuwa da ta.

Hukumar DSS ta bayyana cewa bayan karbar Aisha ‘yar shekara 4 da aka sace tare da wanda ta sace ta, sun gano mutumin da ke safarar kananan yara daga Jihohin Makwafta inda ake sayar da su a Kudancin kasar nan.

“Mun kama babban mai safarar kananan yara daga jihohin makwabta zuwa Kano tare da sayar da su a Kudancin kasar nan.

PRNigeria Hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp