Home General Ba mu muka kama matashin da ya buga rigunan zanga-zanga a Kano...

Ba mu muka kama matashin da ya buga rigunan zanga-zanga a Kano ba – DSS

Ba mu muka kama matashin da ya buga rigunan zanga-zanga a Kano ba – DSS

Hukumar tsaro ta DSS ta musanta labarin da ke cewa jami’anta sun kama wani matashi a jihar Kano da ke sayar da riguna domin shirin gudanar da zanga-zanga kan tsadar rayuwa a Nijeriya ta ‘#EndBadGovernanceInNigeria’.

Tun da fari dai tsohon ɗan takarar Shugaban Kasa karkashin inuwar jam’iyyar AAC a zaben 2023, Omoyele Sowore ne ya wallafa a shafinsa na X a ranar Litinin cewa jami’an DSS din sun kama matashin dan asalin jihar Kano mai suna Bashir Abubakar.

Sowere ya ce DSS a ranar Litinin sun saki guda cikin wadanda suke shirya zanga-zangar ta da za a yi a watan Agusta.

Ya rubuta, “tawagar lauyoyin da aka turawa @OfficialDSSNG sun sami nasarar kubutar da Bashir Abubakar daga hannun jami’an na DSS.

“Bashir matashin dan gwagwarmaya ne daga Kano, wanda ake zargi da samar da riguna masu dauke da rubutun #EndBadGovernanceInNigeria a jihar Kano.”

Sai dai ko da aka tambayi Kakakin hukumar na kasa, Peter Ifunanya kai tsaye ya kada baki ya ce, “ba gaskiya ba ne,” kamar yadda jaridar Daily Post ta ruwaito.

Idan za a iya tunawa ko bayan zanga-zangar kin jinin jami’an tsaro ta #EndARs a Nijeriya, wasu bayanani da jaridar PRNigeria ta tattara wanda ta yi wa lakabi da “101 Fake news on EndSars protest” sun nuna irin tarin karairayin da aka yi amfani da su wajen assasa zanga-zangar wadda ta bar baya da kura a kasar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp