Home General Ba mu muka kama matashin da ya buga rigunan zanga-zanga a Kano...

Ba mu muka kama matashin da ya buga rigunan zanga-zanga a Kano ba – DSS

Ba mu muka kama matashin da ya buga rigunan zanga-zanga a Kano ba – DSS

Hukumar tsaro ta DSS ta musanta labarin da ke cewa jami’anta sun kama wani matashi a jihar Kano da ke sayar da riguna domin shirin gudanar da zanga-zanga kan tsadar rayuwa a Nijeriya ta ‘#EndBadGovernanceInNigeria’.

Tun da fari dai tsohon ɗan takarar Shugaban Kasa karkashin inuwar jam’iyyar AAC a zaben 2023, Omoyele Sowore ne ya wallafa a shafinsa na X a ranar Litinin cewa jami’an DSS din sun kama matashin dan asalin jihar Kano mai suna Bashir Abubakar.

Sowere ya ce DSS a ranar Litinin sun saki guda cikin wadanda suke shirya zanga-zangar ta da za a yi a watan Agusta.

Ya rubuta, “tawagar lauyoyin da aka turawa @OfficialDSSNG sun sami nasarar kubutar da Bashir Abubakar daga hannun jami’an na DSS.

“Bashir matashin dan gwagwarmaya ne daga Kano, wanda ake zargi da samar da riguna masu dauke da rubutun #EndBadGovernanceInNigeria a jihar Kano.”

Sai dai ko da aka tambayi Kakakin hukumar na kasa, Peter Ifunanya kai tsaye ya kada baki ya ce, “ba gaskiya ba ne,” kamar yadda jaridar Daily Post ta ruwaito.

Idan za a iya tunawa ko bayan zanga-zangar kin jinin jami’an tsaro ta #EndARs a Nijeriya, wasu bayanani da jaridar PRNigeria ta tattara wanda ta yi wa lakabi da “101 Fake news on EndSars protest” sun nuna irin tarin karairayin da aka yi amfani da su wajen assasa zanga-zangar wadda ta bar baya da kura a kasar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp