Home General Kunyi zanga zangar 2012 amma kuma zaku hana matasa a yanzu –...

Kunyi zanga zangar 2012 amma kuma zaku hana matasa a yanzu – Atiku

Tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar, ya soki Gwamnatin Tarayya kan ƙoƙarin dakatar da zanga-zangar da ake shirin gudanarwa a Nijeriya saboda matsin rayuwa a ranar 1 ga watan Agusta.

Atiku ya bayyana yunƙurin da abun dariya, saboda waɗanda ke ƙoƙarin hana zanga-zangar su ne waɗanda suka yi wa tsohon Shugaban Ƙasa Goodluck Jonathan zanga-zanga a shekarar 2012.

Zanga-zangar, wadda matasa suka shirya, na da nufin jawo hankali kan ƙaruwar yunwa da wahala da ’yan ƙasa ke fuskanta.

Masu shirya zanga-zangar sun ce za a shafe kwanaki 10 duba da halin matsi da ke ƙara ta’azzara, wanda suka ce akwai buƙatar kulawar gaggawa daga gwamnatin tarayya da na jihohi.

A wani rubutu da ya wallafa a shafinsa na Facebook, Atiku ya jaddada cewa ‘yancin yin zanga-zanga yana cikin kundin tsarin mulkin Najeriya.

Ya buƙaci gwamnati da ta samar da yanayin tsaro da kwanciyar hankali don gudanar da zanga-zangar lumana, saboda ‘yan ƙasa suna da ’yancin gudanar da taro da bayyana ra’ayoyinsu.

Atiku ya soki gwamnati kan ƙoƙarin take waɗannan haƙƙoƙi, inda ya ce wannan ba ba ya cikin doka kuma yana barazana ga dimokuraɗiyya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp