Home General Zanga – Zanga babu gudu ba ja da baya a Kano –...

Zanga – Zanga babu gudu ba ja da baya a Kano – WAI

Ƙungiyar kare haƙƙin Ɗan Adam, yaƙi da rashin adalci dama bibiya akan shugabanci na gari wato War Against Injustice (WAI), ta ce babu gudu babu ja da bayan akan Zanga-zangar da ta ayyana gudanarwa daga ranar 1 ga watan Agusta zuwa 10 ga wata.
Babban daraktan ƙungiyar Kwamared Umar Ibrahim Umar ne ya sanar da hakan ta cikin wani saƙon murya da jaridar GTR HAUSA ta samu a yammacin talata, inda ya ce matakin ya zama dole domin nunawa mahukunta halin da talaka yake ciki.
A cewar Kwamared Umar “Ina wannan magana ne a matsayin martani dangane da taron manema labaran da wata ƙungiya tayi a jiya wadda ta ce sun janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa, adan haka mu bamu janye ba kuma zamu gudanar a ranakun da muka ayyana.
Ya ƙara da cewa zasu gudanar da zanga-zangar tasu cikin lumana da kwanciyar hankali kuma ba tare da taɓa haƙƙin al’umma ba, ta yadda zasu nunawa duniya halinda talakawan ƙasar ke ciki na yunwa, fatara da kuma talaucin da yayi musu katutu.
A ƙarshe ƙungiyar tayi fatan Al’ummar jihar zasu basu haɗin kai da goyon baya domin ayi lafiya kuma a kammala lafiya.
A jiya ne ƙungiyar Shugabannin Matasan Arewacin Najeriya ta ce ta janye zanga-zangar da ta shirya gudanarwa, a sakamakon yadda ta gano akwai masu ƙoƙorin rikita ƙasar ta hanyar amfani da zanga-zangar tasu.
PRNigeria hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp