Home General Zanga – Zanga babu gudu ba ja da baya a Kano –...

Zanga – Zanga babu gudu ba ja da baya a Kano – WAI

Ƙungiyar kare haƙƙin Ɗan Adam, yaƙi da rashin adalci dama bibiya akan shugabanci na gari wato War Against Injustice (WAI), ta ce babu gudu babu ja da bayan akan Zanga-zangar da ta ayyana gudanarwa daga ranar 1 ga watan Agusta zuwa 10 ga wata.
Babban daraktan ƙungiyar Kwamared Umar Ibrahim Umar ne ya sanar da hakan ta cikin wani saƙon murya da jaridar GTR HAUSA ta samu a yammacin talata, inda ya ce matakin ya zama dole domin nunawa mahukunta halin da talaka yake ciki.
A cewar Kwamared Umar “Ina wannan magana ne a matsayin martani dangane da taron manema labaran da wata ƙungiya tayi a jiya wadda ta ce sun janye zanga-zangar da suka shirya gudanarwa, adan haka mu bamu janye ba kuma zamu gudanar a ranakun da muka ayyana.
Ya ƙara da cewa zasu gudanar da zanga-zangar tasu cikin lumana da kwanciyar hankali kuma ba tare da taɓa haƙƙin al’umma ba, ta yadda zasu nunawa duniya halinda talakawan ƙasar ke ciki na yunwa, fatara da kuma talaucin da yayi musu katutu.
A ƙarshe ƙungiyar tayi fatan Al’ummar jihar zasu basu haɗin kai da goyon baya domin ayi lafiya kuma a kammala lafiya.
A jiya ne ƙungiyar Shugabannin Matasan Arewacin Najeriya ta ce ta janye zanga-zangar da ta shirya gudanarwa, a sakamakon yadda ta gano akwai masu ƙoƙorin rikita ƙasar ta hanyar amfani da zanga-zangar tasu.
PRNigeria hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp