DSS da Hisba sun kama masu safarar mutane a Jihar Kano

Hukumar tsaro DSS ta sami nasarar bankado wata kungiyar dake ayyukan fataucin yara kanana a jihar Kano dake Arewa maso Yammacin Nijeriya.

jaridar Solacebase ta ruwaito ofishin cewa Ofishin hukumar na jihar kano ne ya bayyana hakan ranar Talata, inda yace dakarun hukumar sun sami nasarar kama wata mata mai kimanin shekaru 17 da haihuwa tare da kubutar da wata yarinya ýar shekara 4 a duniya daga hannun bata garin wadda ýar asalin Nguru ce a jihar Yobe.

Haka zalika ya kara da cewa Jami’an Hisbah na Jihar Kano sun mika wa wata yarinya ‘yar shekara 4 mai suna A’isha da aka yi garkuwa da ita daga Nguru wadda wata mata ‘yar shekara 17 da aka  sakaya sunanta ta kawo ta Kano bayan sun yi garkuwa da ta.

Hukumar DSS ta bayyana cewa bayan karbar Aisha ‘yar shekara 4 da aka sace tare da wanda ta sace ta, sun gano mutumin da ke safarar kananan yara daga Jihohin Makwafta inda ake sayar da su a Kudancin kasar nan.

“Mun kama babban mai safarar kananan yara daga jihohin makwabta zuwa Kano tare da sayar da su a Kudancin kasar nan.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 26 minutes 29 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 7 minutes 54 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com