Home General Ba mu muka kama matashin da ya buga rigunan zanga-zanga a Kano...

Ba mu muka kama matashin da ya buga rigunan zanga-zanga a Kano ba – DSS

Ba mu muka kama matashin da ya buga rigunan zanga-zanga a Kano ba – DSS

Hukumar tsaro ta DSS ta musanta labarin da ke cewa jami’anta sun kama wani matashi a jihar Kano da ke sayar da riguna domin shirin gudanar da zanga-zanga kan tsadar rayuwa a Nijeriya ta ‘#EndBadGovernanceInNigeria’.

Tun da fari dai tsohon ɗan takarar Shugaban Kasa karkashin inuwar jam’iyyar AAC a zaben 2023, Omoyele Sowore ne ya wallafa a shafinsa na X a ranar Litinin cewa jami’an DSS din sun kama matashin dan asalin jihar Kano mai suna Bashir Abubakar.

Sowere ya ce DSS a ranar Litinin sun saki guda cikin wadanda suke shirya zanga-zangar ta da za a yi a watan Agusta.

Ya rubuta, “tawagar lauyoyin da aka turawa @OfficialDSSNG sun sami nasarar kubutar da Bashir Abubakar daga hannun jami’an na DSS.

“Bashir matashin dan gwagwarmaya ne daga Kano, wanda ake zargi da samar da riguna masu dauke da rubutun #EndBadGovernanceInNigeria a jihar Kano.”

Sai dai ko da aka tambayi Kakakin hukumar na kasa, Peter Ifunanya kai tsaye ya kada baki ya ce, “ba gaskiya ba ne,” kamar yadda jaridar Daily Post ta ruwaito.

Idan za a iya tunawa ko bayan zanga-zangar kin jinin jami’an tsaro ta #EndARs a Nijeriya, wasu bayanani da jaridar PRNigeria ta tattara wanda ta yi wa lakabi da “101 Fake news on EndSars protest” sun nuna irin tarin karairayin da aka yi amfani da su wajen assasa zanga-zangar wadda ta bar baya da kura a kasar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp