Zanga- Zanga: Ministocin Nijeriya sun shiga ganawar sirri

Sakataren Gwamnatin tarayya, George Akume ya shiga ganawa da ministoci a yayin da ake shirin fara zanga-zanga kan tsadar rayuwa a fadin Najeriya.

Ganawar wacce ke gudana cikin sirri ta samu halartar ministoci sama da 40 na gwamnatin shugaba Tinubu.

Wasu daga cikin ministocin da aka hango a wajen ganawar sun hada da: Nyesom Wike na birnin tarayya Abuja da ministan harkokin wajen Najeriya, Yusuf Tuggar da Zephnia Jisalo da Tahir Mamman da Atiku Bagudu.

Sauran ministocin sun hada da Wale Edun na kudi da ministan yada labarai Mohammed Idris da sauransu.

wannan dai na  zuwa ne bayan, shugaban kasa Tinubu ya roki matasan Najeriya da su dakata daga shiga zanga zangar ta ‘EndBadGovernance’ da aka tsara farawa a wata mai kamawa.

ko da yake wasu wata kungiya da tayi ikirarin shirya zanga zangar tun da fari a Arewacin kasar ta janye yayin da wata kungiya kuma a jihar kano tace zanga – zanga babu fashi

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 26 minutes 31 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 7 minutes 56 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com