Home General Ya kamata gwamnatin Najeriya ta kare masu saka jari na cikin gida...

Ya kamata gwamnatin Najeriya ta kare masu saka jari na cikin gida – MAN

Ƙungiyar masu masana’antu ta Najeriya ta yi gagaɗi ga gwamnatin ƙasar kan ƙoƙarin gurgunta masana’antun cikin gida.

Ƙungiyar ta yi kiran yin taka-tsantsan da masu ruwa da tsaki kan harakar man fetur da kuma hukumomi sakamakon rikicin gwamnatin tarayya da Matatar Dangote.

Babban Daraktan ƙungiyar Ajayi Kabir ya ce hukumomin gwamnati da ke aikin sa-ido yakamata su inganta yanayi mai kyau na kasuwanci da zuba jari comin ci gaban masana’antun cikin gida.

Ya ce babu wata hukuma da ta kamata ta kawo tarnaki ga babbar masana’anta ta cikin gida kamar Matatar Dangote.

Ya ƙara da cewa masu zuba jari na cikin gida a Najeriya kamar Matatar Dangote suna taka rawa sosai wajen bunƙasa tattalin arziki da biyan haraji da samar da ayyukan yi da kuma ci gaba. Don haka a cewarsa ya kamata a ba su goyon bayan da suke buƙata domin ci gaban kasuwancinsu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp