Home General Ya kamata gwamnatin Najeriya ta kare masu saka jari na cikin gida...

Ya kamata gwamnatin Najeriya ta kare masu saka jari na cikin gida – MAN

Ƙungiyar masu masana’antu ta Najeriya ta yi gagaɗi ga gwamnatin ƙasar kan ƙoƙarin gurgunta masana’antun cikin gida.

Ƙungiyar ta yi kiran yin taka-tsantsan da masu ruwa da tsaki kan harakar man fetur da kuma hukumomi sakamakon rikicin gwamnatin tarayya da Matatar Dangote.

Babban Daraktan ƙungiyar Ajayi Kabir ya ce hukumomin gwamnati da ke aikin sa-ido yakamata su inganta yanayi mai kyau na kasuwanci da zuba jari comin ci gaban masana’antun cikin gida.

Ya ce babu wata hukuma da ta kamata ta kawo tarnaki ga babbar masana’anta ta cikin gida kamar Matatar Dangote.

Ya ƙara da cewa masu zuba jari na cikin gida a Najeriya kamar Matatar Dangote suna taka rawa sosai wajen bunƙasa tattalin arziki da biyan haraji da samar da ayyukan yi da kuma ci gaba. Don haka a cewarsa ya kamata a ba su goyon bayan da suke buƙata domin ci gaban kasuwancinsu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp