Home General NLC ta musanta Janyewar shiga Zanga Zanga a Nijeriya

NLC ta musanta Janyewar shiga Zanga Zanga a Nijeriya

Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya (NLC), ta ce bata janye daga shiga zanga-zangar matsin rayuwar da ake shirin gudanarwa a ƙasar ba.

Ƙungiyar ta sanar da hakan ne ta cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X, inda ta barranta kanta da labarin da ake yaɗawa na cewa ta fasa shiga zanga-zangar.
Sanarwar da Shugaban Ƙungiyar na ƙasa Kwamared Joe Ajaero ya sanyawa hannu ta ƙara da cewa, duk da ba ƙungiyar ce ta shirya zanga-zangar ba amma hakan bazai hana ta shiga ba, saboda halin ƙunci da matsin da talakawan ƙasar suke ciki a sakamakon wasu matakan da gwamnatin ƙasar ta ɗauka.
Adan haka ne ƙungiyar za ta shiga zanga-zangar domin taya al’ummar ƙasar wannan yaƙi, na nema wa kansu sauƙi a cikin mummunan halin da suke ciki.
Haka kuma ta buƙaci Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya zauna da masu shirya zanga-zangar a teburin sulhu, dangane da buƙatun da suke dashi ta yadda za’a magance matsalar ba tare amfani da ƙarfin mulki ba.
A ƙarshe ƙungiyar tayi fatan Gwamnatin tarayya dana jihohi zasu waiwayi koken ‘yan ƙasar, kuma su biya musu dukkan buƙatun su domin gudun faɗawar ƙasar cikin yanayi da ba’a tsammani.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp