Home General NLC ta musanta Janyewar shiga Zanga Zanga a Nijeriya

NLC ta musanta Janyewar shiga Zanga Zanga a Nijeriya

Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya (NLC), ta ce bata janye daga shiga zanga-zangar matsin rayuwar da ake shirin gudanarwa a ƙasar ba.

Ƙungiyar ta sanar da hakan ne ta cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na X, inda ta barranta kanta da labarin da ake yaɗawa na cewa ta fasa shiga zanga-zangar.
Sanarwar da Shugaban Ƙungiyar na ƙasa Kwamared Joe Ajaero ya sanyawa hannu ta ƙara da cewa, duk da ba ƙungiyar ce ta shirya zanga-zangar ba amma hakan bazai hana ta shiga ba, saboda halin ƙunci da matsin da talakawan ƙasar suke ciki a sakamakon wasu matakan da gwamnatin ƙasar ta ɗauka.
Adan haka ne ƙungiyar za ta shiga zanga-zangar domin taya al’ummar ƙasar wannan yaƙi, na nema wa kansu sauƙi a cikin mummunan halin da suke ciki.
Haka kuma ta buƙaci Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya zauna da masu shirya zanga-zangar a teburin sulhu, dangane da buƙatun da suke dashi ta yadda za’a magance matsalar ba tare amfani da ƙarfin mulki ba.
A ƙarshe ƙungiyar tayi fatan Gwamnatin tarayya dana jihohi zasu waiwayi koken ‘yan ƙasar, kuma su biya musu dukkan buƙatun su domin gudun faɗawar ƙasar cikin yanayi da ba’a tsammani.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp