Tinubu zai samawa ‘yan sandan Nijeriya karin makamai

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya jaddada aniyar sa ta samawa dakarun ‘yan sandan kasar makamai da daukar’ karin jami’ai domin yaki da laifuka a kasar.

Shugaban kasar ya bayyana hakan ne a yayin gudanar da bikin kaddamar da sashen yaki da laifukan internet a binrin tarayya Abuja ranar laraba, inda ya bayyana manufarsa ta kawo karshen ayyukan hadakar jami’an tsakanin hukumomi a kasar.

Yace ya fahimci laifukan zambar kafar Internet ya kara karuwa a kasar, yace abu ne da baya bukatar hadin gwiwa tsakanin hukumomin domin magance matsalar.

Da yake jawabi a wajen taron Shugaban kasa Bola Tinubu wanda ya sami wakilcin ministan sadarwa da tattalin arziki na zamani, Bossum Tijani, yace yanayin tsaro a kasar yayi tsamari lamarin dake bukatar sake zage dantse domin magance matsalar.

Tinubu ya tabbatarwa da Al’ummar Nijeriya cewa gwamnatinsa zata yi dukkan mai yiwuwa wajen sanya makudan kudi don gani ta samawa jami’an ‘yan sandan makamai

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 40 minutes 29 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 21 minutes 54 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com