Home DUNIYA Shugaban Chaina ya yaba da kamun Ludayin Tinubu a ECOWAS

Shugaban Chaina ya yaba da kamun Ludayin Tinubu a ECOWAS

Shugaban ƙasar China Xi Jinping, ya gayyaci takwaransa na Najeriya Bola Tinubu, domin kai ziyarar aiki ƙasar.

Wannan na cikin wata sanarwa da kakakin shugaban kasar, Ajuri Ngelale ya fitar, wadda ta ce mataimakin ministan ƙasashen wajen China, Chen Xiaodong, ne ya je da saƙon gayyatar ca wata ziyara da ya kai Najeriya.

Mista Xiaodong ya yaba wa Shugaba Tinubu kan irin tsare-tsarensa, da irin rawar da shugaban ke takawa a matsayinsa na jagoran kungiyar Ecowas.

“Kai shugaba ne mai haƙaza da fikira. Mun yi imanin cewa ganawar ka da Mista Jinping zai kawo damarmaki masu yawa ga Najeriya da Afirka,’’ in ji shi.

A nasa ɓangaren shugaban na Najeriya ya yaba wa shugaban China, bisa ƙoƙarin da yake yi na ƙarfafa alaƙa da Najeriya da ƙasashen nahiyar Afirka.

“Mun yi imani da alaƙar da ke tsakaninmu, kuma muna son yauƙaƙa danƙon zumuncin da ke tsakaninmu , musamman ta hukumomin MDD da ƙungiyar BRICS da G20.”, in ji sanarwar.

Haka kuma shugaban ya yaba da saƙon gayyatar da shugaban na China ya aika masa na ziyarar aiki zuwa China.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp