Home DUNIYA An kai hari tare da lalata wasu muhimman layukan jiragen ƙasa a...

An kai hari tare da lalata wasu muhimman layukan jiragen ƙasa a Faransa

Kamfanin dake kula da  sufurin jiragen ƙasa na Faransa  SNCF, ya ce wasu da ba a san ko su waye ba, sun kai hari tare da lalata sassan titunan jirage masu tsala gudu, yayin da ya rage sa’o’i kaɗan a buɗe gasar wasannin Olympics da birnin Paris ke karɓar baƙunci.

Yayin zantawa da kamfanin dillancin labarai na AFP, kamfanin na SNCF ya bayyana farmakin a matsayin babbar barazana, la’akari da tasirin da ya riga yayi, domin tilas aka soke jigilar jiragen ƙasa zuwa sassan Faransa da dama, wanda kuma sai an shafe hutun ƙarshen mako kafin kammala gyara layukan dogon da aka lalata.

Kamfanin kula da sufurin jiragen ƙasan na Faransar ya shawarci fasinjoji da su ɗage lokutan da suka tsara na yin balaguro, su kuma ƙauracewa zuwa tashohin jiragen ƙasa har zuwa lokacin da za a tabbatar da tsaro.

Harin dai yafi shafar titunan jiragen ƙasan masu tsala gudu da ke jigila zuwa yankunan Arewaci da Gabashin ƙasar, yayin da jami’an tsaro suka daƙile yunƙurin da aka yi na lalata titunan da ke sadarwa zuwa yankin Kudu maso Gabashi.

Kimanin ‘yan wasa 7,500 ake sa ran sun hallara a birnin Paris domin nuna bajintarsu a gasar Olympics, yayin da ake kiyasta yawan ‘yan kallo zai kai dubu 300.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp