Home DUNIYA An kai hari tare da lalata wasu muhimman layukan jiragen ƙasa a...

An kai hari tare da lalata wasu muhimman layukan jiragen ƙasa a Faransa

Kamfanin dake kula da  sufurin jiragen ƙasa na Faransa  SNCF, ya ce wasu da ba a san ko su waye ba, sun kai hari tare da lalata sassan titunan jirage masu tsala gudu, yayin da ya rage sa’o’i kaɗan a buɗe gasar wasannin Olympics da birnin Paris ke karɓar baƙunci.

Yayin zantawa da kamfanin dillancin labarai na AFP, kamfanin na SNCF ya bayyana farmakin a matsayin babbar barazana, la’akari da tasirin da ya riga yayi, domin tilas aka soke jigilar jiragen ƙasa zuwa sassan Faransa da dama, wanda kuma sai an shafe hutun ƙarshen mako kafin kammala gyara layukan dogon da aka lalata.

Kamfanin kula da sufurin jiragen ƙasan na Faransar ya shawarci fasinjoji da su ɗage lokutan da suka tsara na yin balaguro, su kuma ƙauracewa zuwa tashohin jiragen ƙasa har zuwa lokacin da za a tabbatar da tsaro.

Harin dai yafi shafar titunan jiragen ƙasan masu tsala gudu da ke jigila zuwa yankunan Arewaci da Gabashin ƙasar, yayin da jami’an tsaro suka daƙile yunƙurin da aka yi na lalata titunan da ke sadarwa zuwa yankin Kudu maso Gabashi.

Kimanin ‘yan wasa 7,500 ake sa ran sun hallara a birnin Paris domin nuna bajintarsu a gasar Olympics, yayin da ake kiyasta yawan ‘yan kallo zai kai dubu 300.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp