Home DUNIYA Shugaban Chaina ya yaba da kamun Ludayin Tinubu a ECOWAS

Shugaban Chaina ya yaba da kamun Ludayin Tinubu a ECOWAS

Shugaban ƙasar China Xi Jinping, ya gayyaci takwaransa na Najeriya Bola Tinubu, domin kai ziyarar aiki ƙasar.

Wannan na cikin wata sanarwa da kakakin shugaban kasar, Ajuri Ngelale ya fitar, wadda ta ce mataimakin ministan ƙasashen wajen China, Chen Xiaodong, ne ya je da saƙon gayyatar ca wata ziyara da ya kai Najeriya.

Mista Xiaodong ya yaba wa Shugaba Tinubu kan irin tsare-tsarensa, da irin rawar da shugaban ke takawa a matsayinsa na jagoran kungiyar Ecowas.

“Kai shugaba ne mai haƙaza da fikira. Mun yi imanin cewa ganawar ka da Mista Jinping zai kawo damarmaki masu yawa ga Najeriya da Afirka,’’ in ji shi.

A nasa ɓangaren shugaban na Najeriya ya yaba wa shugaban China, bisa ƙoƙarin da yake yi na ƙarfafa alaƙa da Najeriya da ƙasashen nahiyar Afirka.

“Mun yi imani da alaƙar da ke tsakaninmu, kuma muna son yauƙaƙa danƙon zumuncin da ke tsakaninmu , musamman ta hukumomin MDD da ƙungiyar BRICS da G20.”, in ji sanarwar.

Haka kuma shugaban ya yaba da saƙon gayyatar da shugaban na China ya aika masa na ziyarar aiki zuwa China.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp