Home General ”Arewa Media Writers” ta umarci mambobinta su fito Zanga Zanga

”Arewa Media Writers” ta umarci mambobinta su fito Zanga Zanga

Ƙungiyar Marubutan Arewa a Kafofin sadarwa na zamani wato Arewa Media Writers, ta umarci dukkan Mambobinta na Jihohi 19 har da Abuja su fito Zanga-zangar lumana a ranar Alhamis 1 ga watan Augusta.

Ƙungiyar ta sanar da hakan ne ta cikin wata sanarwa da Mataimakin Daraktan yaɗa labaranta na ƙasa Muhammad Kwairi Waziri ya aiko wa manema labarai a safiyar yau Litinin. inda ta ce ya zama wajibi su fito domin ƙara sanar da gwamnati matsalolin da ake fuskanta a yankin Arewa.

Sanarwar ƙungiyar ta ƙara da cewa al’ummar Arewa suna cikin matslolin rashin tsaro, yunwa, tsadar rayuwa, amma kuma gwamnati ta kasa magance musu matsalolin.

Haka zalika ƙungiyar ta ƙara jaddada wa magoya bayanta cewa babu fitowa da makami ko cin zarafin wani, ko ɗaukar kayan wani a yayin zanga-zangar, wanda dama ba fito na fito za’ai da gwamnati ba, illa kira ga hukuma da su san halin matsi da ƙuncin da al’umma suke ciki.

A ƙarshe ta yi kira ga dukkan masu fitowa zanga-zangar da su bawa jami’an tsaro haɗin kai yayin fitar, kuma su kula da bin doka da oda ta ƙasa Nijeriya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp