Home General Mene yasa Amurka, Birtaniya da Canada suka gargadi al’ummarsu kan zanga-zanga a...

Mene yasa Amurka, Birtaniya da Canada suka gargadi al’ummarsu kan zanga-zanga a Najeriya

Amurka da Birtaniya da Canada sun buƙaci al’ummarsu da ke zaune a Najeriya su zama masu taka-tsan-tsan inda suka yi gargaɗin yiwuwar samun tashin hankali a zanga-zangar gama-garin da ake shirin yi.

Gargaɗin ya so ne daidai lokacin da al’ummar ƙasar ke shirya zanga-zanga don nuna tura ta kai bango ga matsalolin yunwa da kuma matsin rayuwa da aka tsara somawa ranar 1 ga watan Agusta.

A wasu shawarwari da ƙasashen suka bai wa al’ummarsu da ke zaune a Najeriya, sun buƙace su da su guji wuraren da za a iya samun arangama tsakanin jami’an tsaro da masu zanga-zangar.

A na shi shawarar, ofishin jakadancin Amurka da ke Abuja ya buƙaci Amurkawa da su nesanta kansu daga gangamin inda suka shawarce su da su kaucewa shiga dandazon jama’a su kuma ƙauracewa zanga-zanga sannan su kuma riƙa sauraron labarai.

Haka zalika, ofishin jakadancin Birtaniya a Najeriyar ya yi gargaɗi cewa za a yi ganin zanga-zangar tsakanin yau 29 ga watan Yuli zuwa 10 ga watan Agusta a manyan birane kamar Abuja da Legas.

Ofishin ya buƙaci al’ummar Birtaniyar su yi kaffa-kaffa sannan su guji wuraren taron jama’a inda suka yi misali da yadda zanga-zangar da aka yi a baya ta rikiɗe zuwa tashin hankali.

Ita ma gwamnatin Canada ta shawarci al’ummarta da su bi umarnin hukumomi su kuma ci gaba da bibiyar kakafen yaɗa labarai domin sanin abin da ke wakana.

Wannan dai na nuna yadda ake nuna fargaba kan al’amura a Najeriya game da zanga-zangar da ake shirin yi da kuma tasirinta kan tsaron Najeriya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp