Home General ”Arewa Media Writers” ta umarci mambobinta su fito Zanga Zanga

”Arewa Media Writers” ta umarci mambobinta su fito Zanga Zanga

Ƙungiyar Marubutan Arewa a Kafofin sadarwa na zamani wato Arewa Media Writers, ta umarci dukkan Mambobinta na Jihohi 19 har da Abuja su fito Zanga-zangar lumana a ranar Alhamis 1 ga watan Augusta.

Ƙungiyar ta sanar da hakan ne ta cikin wata sanarwa da Mataimakin Daraktan yaɗa labaranta na ƙasa Muhammad Kwairi Waziri ya aiko wa manema labarai a safiyar yau Litinin. inda ta ce ya zama wajibi su fito domin ƙara sanar da gwamnati matsalolin da ake fuskanta a yankin Arewa.

Sanarwar ƙungiyar ta ƙara da cewa al’ummar Arewa suna cikin matslolin rashin tsaro, yunwa, tsadar rayuwa, amma kuma gwamnati ta kasa magance musu matsalolin.

Haka zalika ƙungiyar ta ƙara jaddada wa magoya bayanta cewa babu fitowa da makami ko cin zarafin wani, ko ɗaukar kayan wani a yayin zanga-zangar, wanda dama ba fito na fito za’ai da gwamnati ba, illa kira ga hukuma da su san halin matsi da ƙuncin da al’umma suke ciki.

A ƙarshe ta yi kira ga dukkan masu fitowa zanga-zangar da su bawa jami’an tsaro haɗin kai yayin fitar, kuma su kula da bin doka da oda ta ƙasa Nijeriya.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp