Home General Jami’oi ku lura da Lafiyar Dalibai da Ma’aikatan ku yayin zanga-zanga –...

Jami’oi ku lura da Lafiyar Dalibai da Ma’aikatan ku yayin zanga-zanga – Ministan Ilimi

Gwamantin Nijeriya ta umarci Jami’oin kasar da su Tabbatar da tsaron Lafiyar dalibai da kuma maáikata a makarantunsu yayin da ake gudanar da zanga-zangar.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da mukaddashin shugaban hukumar kula da jami’oin kasar, Chris Maiyaki ya fitar wacce aka rabawa manema labarai a yau Litinin bias umarnin ministan ilimin kasar Farfesa Tahir Mamman.

Wannan dai na zuwa ne daidai lokacin da matasa a Nijeirya ke shirin fitowa titinu domin nuna bakin ciki da haln kuncin rayuwa da suke ciki a kasar, dake da arzikin man Fetur da tarin ma’adanai.

Ta cikin sanarwar Ministan ya kuma bukaci dalibai da su kasance a makarantunsu tare da mayar da hankali ga karatunsu domin kaucewa fadawa hatsari a yayin zanga zangar.

“Gwamnatin tarayya tana sane da hakkin da kowanne dan Nijeriya ke da shi wajen gudanar da zanga zangar lumana, amma mun damu da lafiyar ma’aikata da dalibai da makarantu a yayin zanga-zanga.

” A don haka minista ya umarci dukkan shugabannin makarantu da su dau matakai don tabbatar da tsaron dalibai da ma’aikatan jami’a”.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp