Home General Jami’oi ku lura da Lafiyar Dalibai da Ma’aikatan ku yayin zanga-zanga –...

Jami’oi ku lura da Lafiyar Dalibai da Ma’aikatan ku yayin zanga-zanga – Ministan Ilimi

Gwamantin Nijeriya ta umarci Jami’oin kasar da su Tabbatar da tsaron Lafiyar dalibai da kuma maáikata a makarantunsu yayin da ake gudanar da zanga-zangar.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da mukaddashin shugaban hukumar kula da jami’oin kasar, Chris Maiyaki ya fitar wacce aka rabawa manema labarai a yau Litinin bias umarnin ministan ilimin kasar Farfesa Tahir Mamman.

Wannan dai na zuwa ne daidai lokacin da matasa a Nijeirya ke shirin fitowa titinu domin nuna bakin ciki da haln kuncin rayuwa da suke ciki a kasar, dake da arzikin man Fetur da tarin ma’adanai.

Ta cikin sanarwar Ministan ya kuma bukaci dalibai da su kasance a makarantunsu tare da mayar da hankali ga karatunsu domin kaucewa fadawa hatsari a yayin zanga zangar.

“Gwamnatin tarayya tana sane da hakkin da kowanne dan Nijeriya ke da shi wajen gudanar da zanga zangar lumana, amma mun damu da lafiyar ma’aikata da dalibai da makarantu a yayin zanga-zanga.

” A don haka minista ya umarci dukkan shugabannin makarantu da su dau matakai don tabbatar da tsaron dalibai da ma’aikatan jami’a”.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp