Home General Sojoji Nijeriya sun mamaye manyan titunan Abuja gabanin zanga-zanga a kasar

Sojoji Nijeriya sun mamaye manyan titunan Abuja gabanin zanga-zanga a kasar

Direbobi a kan babbar hanyar Keffi zuwa Abuja a ranar Litinin sun shiga tsaka mai wuya bayan da sojoji suka tare babbar hanyar domin gudanar da bincike kan motocin da suka nufi Abuja, babban birnin Najeriya.

Sojojin sun dasa shingen bincike a barikin sojoji na Sani Abacha kafin shataletalen AYA.

Jami’an tsaro dai ba su bayar da wata sanarwa ba kafin toshe titin lamarin da ya janyo cunkoson ababen hawa har zuwa gadar Nyanya, sama da kilomita 12 daga wurin binciken motocin.

Jaridar Emergency Digest ta ruwaito cewa ma’aikata da masu tireda da ke aiki a Abuja, suna zaune a wajen tsakiyar birnin a wurare kamar Nyanya da Karu da Maraba da Masaka.

Bayan shafe tsawon sa’oi a wuri ɗaya – babu gaba, babu baya, akasarinsu daga bisani sun yanke shawarar komawa gida.

Wasu matasa a Najeriya na shirya zanga-zangar gama-gari daga 1 ga watan Agusta saboda tsadar rayuwa da taɓarɓarewar tattalin arziki a ƙasar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp