Home General Jami’oi ku lura da Lafiyar Dalibai da Ma’aikatan ku yayin zanga-zanga –...

Jami’oi ku lura da Lafiyar Dalibai da Ma’aikatan ku yayin zanga-zanga – Ministan Ilimi

Gwamantin Nijeriya ta umarci Jami’oin kasar da su Tabbatar da tsaron Lafiyar dalibai da kuma maáikata a makarantunsu yayin da ake gudanar da zanga-zangar.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da mukaddashin shugaban hukumar kula da jami’oin kasar, Chris Maiyaki ya fitar wacce aka rabawa manema labarai a yau Litinin bias umarnin ministan ilimin kasar Farfesa Tahir Mamman.

Wannan dai na zuwa ne daidai lokacin da matasa a Nijeirya ke shirin fitowa titinu domin nuna bakin ciki da haln kuncin rayuwa da suke ciki a kasar, dake da arzikin man Fetur da tarin ma’adanai.

Ta cikin sanarwar Ministan ya kuma bukaci dalibai da su kasance a makarantunsu tare da mayar da hankali ga karatunsu domin kaucewa fadawa hatsari a yayin zanga zangar.

“Gwamnatin tarayya tana sane da hakkin da kowanne dan Nijeriya ke da shi wajen gudanar da zanga zangar lumana, amma mun damu da lafiyar ma’aikata da dalibai da makarantu a yayin zanga-zanga.

” A don haka minista ya umarci dukkan shugabannin makarantu da su dau matakai don tabbatar da tsaron dalibai da ma’aikatan jami’a”.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp