Home General Mene yasa Amurka, Birtaniya da Canada suka gargadi al’ummarsu kan zanga-zanga a...

Mene yasa Amurka, Birtaniya da Canada suka gargadi al’ummarsu kan zanga-zanga a Najeriya

Amurka da Birtaniya da Canada sun buƙaci al’ummarsu da ke zaune a Najeriya su zama masu taka-tsan-tsan inda suka yi gargaɗin yiwuwar samun tashin hankali a zanga-zangar gama-garin da ake shirin yi.

Gargaɗin ya so ne daidai lokacin da al’ummar ƙasar ke shirya zanga-zanga don nuna tura ta kai bango ga matsalolin yunwa da kuma matsin rayuwa da aka tsara somawa ranar 1 ga watan Agusta.

A wasu shawarwari da ƙasashen suka bai wa al’ummarsu da ke zaune a Najeriya, sun buƙace su da su guji wuraren da za a iya samun arangama tsakanin jami’an tsaro da masu zanga-zangar.

A na shi shawarar, ofishin jakadancin Amurka da ke Abuja ya buƙaci Amurkawa da su nesanta kansu daga gangamin inda suka shawarce su da su kaucewa shiga dandazon jama’a su kuma ƙauracewa zanga-zanga sannan su kuma riƙa sauraron labarai.

Haka zalika, ofishin jakadancin Birtaniya a Najeriyar ya yi gargaɗi cewa za a yi ganin zanga-zangar tsakanin yau 29 ga watan Yuli zuwa 10 ga watan Agusta a manyan birane kamar Abuja da Legas.

Ofishin ya buƙaci al’ummar Birtaniyar su yi kaffa-kaffa sannan su guji wuraren taron jama’a inda suka yi misali da yadda zanga-zangar da aka yi a baya ta rikiɗe zuwa tashin hankali.

Ita ma gwamnatin Canada ta shawarci al’ummarta da su bi umarnin hukumomi su kuma ci gaba da bibiyar kakafen yaɗa labarai domin sanin abin da ke wakana.

Wannan dai na nuna yadda ake nuna fargaba kan al’amura a Najeriya game da zanga-zangar da ake shirin yi da kuma tasirinta kan tsaron Najeriya.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp