Tinubu ya bawa NNPCL Umarni kan Matatar Dangote

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya umarci kamfanin man fetur na kasar daya sayarwa da matatar Mai ta Dangode Danyen Man fetur da sauran matatun cikin gida da naira ba da dalar Amurka ba.

shugaban hukumar tattara haraji ta Gwamantin tarayya (FIRS) Zack Adedeji ne ya bayyana hakan jim kadan bayan fitowa daga taron majalisar zartarwa kasar data gudanar ranar litini, bisa jagorancin shugaban kasar Asiwaju Bola Ahmad Tinubu a birnin Abuja.

Adedeji yace matakin zai taimakawa kasar wajen rage dogaro da dalar Amurka da tayi, sannan kuma zai rage tsadar farashin man fetur da man Diesel da sauran dangoginsu a gidajen Man dake kasar.

ya kara da majalisar zartarwa ta umarci dukkan kamfanin na jihohin kasar dasu fara aiwatar da ita nan take domin habaka harkokin man a fadin Nijeriya.

haka kuma shugaban hukuma FIRs yace sayar da tacen man fetur din daga Matatar ta Dangote zai kasance ne da Naira ba da Dalar Amurka ba.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 6 minutes 38 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 10 hours 48 minutes 3 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com