Home General NCC ta bayar da Umarnin bude layukan da aka rufe a Nijeriya

NCC ta bayar da Umarnin bude layukan da aka rufe a Nijeriya

Hukumar kula da kamfanonin sadarwa ta Najeriya ta umarci kamfanonin sadarwa da su gaggauta buɗe layukan wayoyin da aka rufe saboda rashin haɗa layukan da lambar ɗan ƙasa ta NIN.

Darakta yaɗa labarai na hukumar, Reuben Muoka ne ya bayyana haka ranar Litinin, ta cikin wata sanarwa da NCC ta fitar, ya ce abokanan hulɗar kamfanonin ba sa iya amfani da layukan nasu saboda sun gaza haɗa lambobinsu na NIN da layukan wayoyinsu.

Sanarwar ta ce a ƙarshen makon nan ne, masu amfani da layukan sadarwa suka fuskanci ƙalubale wajen amfani da layukan wayoyinsu saboda rashin haɗa lambobinsu na NIN da layukansu.

“Hakan ya sa an toshe layuka da dama bisa dokoki da ƙa’idojin jaɗa NIN da layukan waya.” in ji sanarwar.

Tun Disambar 2023, hukumar ta NCC ta ke nazari kan wa’adin da aka ɗiba na haɗa NIN da layukan waya, an saka 15 ga watan Afrilu a matsayin wa’adin rufe layukan da ba a haɗa su da lambar NIN ba.

An kuma sake tsawaita wa’adin zuwa 31 ga Yulin 2024 domin bai wa kwastamomi dama su miƙa lambobinsu na NIN domin a tantance.

Sai dai duk da tswaita wa’adin, wasu layukan ba a haɗa su da NIN ba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp