Home General NCC ta bayar da Umarnin bude layukan da aka rufe a Nijeriya

NCC ta bayar da Umarnin bude layukan da aka rufe a Nijeriya

Hukumar kula da kamfanonin sadarwa ta Najeriya ta umarci kamfanonin sadarwa da su gaggauta buɗe layukan wayoyin da aka rufe saboda rashin haɗa layukan da lambar ɗan ƙasa ta NIN.

Darakta yaɗa labarai na hukumar, Reuben Muoka ne ya bayyana haka ranar Litinin, ta cikin wata sanarwa da NCC ta fitar, ya ce abokanan hulɗar kamfanonin ba sa iya amfani da layukan nasu saboda sun gaza haɗa lambobinsu na NIN da layukan wayoyinsu.

Sanarwar ta ce a ƙarshen makon nan ne, masu amfani da layukan sadarwa suka fuskanci ƙalubale wajen amfani da layukan wayoyinsu saboda rashin haɗa lambobinsu na NIN da layukansu.

“Hakan ya sa an toshe layuka da dama bisa dokoki da ƙa’idojin jaɗa NIN da layukan waya.” in ji sanarwar.

Tun Disambar 2023, hukumar ta NCC ta ke nazari kan wa’adin da aka ɗiba na haɗa NIN da layukan waya, an saka 15 ga watan Afrilu a matsayin wa’adin rufe layukan da ba a haɗa su da lambar NIN ba.

An kuma sake tsawaita wa’adin zuwa 31 ga Yulin 2024 domin bai wa kwastamomi dama su miƙa lambobinsu na NIN domin a tantance.

Sai dai duk da tswaita wa’adin, wasu layukan ba a haɗa su da NIN ba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp