Home General NCC ta bayar da Umarnin bude layukan da aka rufe a Nijeriya

NCC ta bayar da Umarnin bude layukan da aka rufe a Nijeriya

Hukumar kula da kamfanonin sadarwa ta Najeriya ta umarci kamfanonin sadarwa da su gaggauta buɗe layukan wayoyin da aka rufe saboda rashin haɗa layukan da lambar ɗan ƙasa ta NIN.

Darakta yaɗa labarai na hukumar, Reuben Muoka ne ya bayyana haka ranar Litinin, ta cikin wata sanarwa da NCC ta fitar, ya ce abokanan hulɗar kamfanonin ba sa iya amfani da layukan nasu saboda sun gaza haɗa lambobinsu na NIN da layukan wayoyinsu.

Sanarwar ta ce a ƙarshen makon nan ne, masu amfani da layukan sadarwa suka fuskanci ƙalubale wajen amfani da layukan wayoyinsu saboda rashin haɗa lambobinsu na NIN da layukansu.

“Hakan ya sa an toshe layuka da dama bisa dokoki da ƙa’idojin jaɗa NIN da layukan waya.” in ji sanarwar.

Tun Disambar 2023, hukumar ta NCC ta ke nazari kan wa’adin da aka ɗiba na haɗa NIN da layukan waya, an saka 15 ga watan Afrilu a matsayin wa’adin rufe layukan da ba a haɗa su da lambar NIN ba.

An kuma sake tsawaita wa’adin zuwa 31 ga Yulin 2024 domin bai wa kwastamomi dama su miƙa lambobinsu na NIN domin a tantance.

Sai dai duk da tswaita wa’adin, wasu layukan ba a haɗa su da NIN ba.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp