Jami’an tsaro sun yi arangama da masu Zanga-Zanga a jihar Kano

Wasu bayanai daga unguwar bachirawa a jihar Kano na bayyana cewa an yi arangama tsakanin matasan dake fakewa da zanga- zangar tsadar rayuwa suna fasa shaguna da dukiyoyin Al’umma a jihar da jami’an tsaro.

Matasan dai na kokarin kutsawa wani katafaren wurin sayar da kayan masarufi dana kwalam da makwalashe, wannan ne yasa dakarun ‘yan sandan daukar matakin dakile yunkurin nasu abinda ya kai ga harbin wasu daga cikin masu fakewa da zanga zangar.

Tun dai da sanyi safiya matasan suka fito domin sake dorawa daga inda aka tsaya a zangar da gwamnatin jihar ta dakatar da ita ta hanyar saka dokar hana fita, bayan ta zargi wasu manyan mutane a jihar da haifar da tarzoma a cikin ta.

Wakilin PRNigeria ya zaga yankin ya tattauna da wasu mutane da lamarin ya auku a gaban idon su, wanda suka ce har an sami asarar rayuka.

Mun yi kokarin tuntubar kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Kano Abdullahi Haruna Kiyawa domin jin yadda lamarin yake, amma bai sami damar amsa kiran ba.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1187 days 17 hours 52 minutes 6 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1169 days 19 hours 33 minutes 31 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com