Home Labarai WAI na shirin kai gwamnatin Nijeriya kara gaban kotun ECOWAS

WAI na shirin kai gwamnatin Nijeriya kara gaban kotun ECOWAS

Ƙungiyar kare haƙƙin dan Adam, yaƙi da rashin adalci dama bibiya akan shugabanci nagari wato War Against Injustice (WAI), ta bayyana shirinta na maka Gwamnatin Najeriya a Kotun ECOWAS nan bada jimawa ba.
Babban Daraktan ƙungiyar Kwamared Umar Ibrahim Umar ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da ya aiko wa manema labarai a Lahadi, biyo bayan Jawabin da Shugaban ƙasar Bola Tinubu yayi wanda ya nuna rashin damuwa da halin da Talakawan ƙasar ke ciki.
A cewar sa “Dole mu ɗauki wannan mataki a sakamakon yadda Gwamnatin ta yi burus da buƙatun da Al’ummar ƙasar suka gabatar mata a wannan lokaci na zanga-zanga, harma Jami’an tsaro suke cin zarafin ‘yan ƙasar dama kashe su”.
Haka kuma ya buƙaci jami’an tsaro suyi gaggawar kama ‘yan Siyasar da suka ɗauki nauyin ɓata zanga-zangar, ta hanyar hayo ‘yan dabar da suka farwa dukiyar al’umma dama kayan Gwamnati.
Bugu da ƙari ƙungiyar ta yi Allah-wadai da cin zarafin ‘yan Jaridar da aka yi a lokacin zanga-zangar, suna tsaka da aikin su na hidimtawa al’umma dama ƙasar gaba-ɗaya.
A ƙarshe ƙungiyar ta yi fatan dukkan ɓangarorin da suke da alaƙa da matakin da suke shirin ɗauka zasu basu haɗin kan da ya kamata, domin nemowa waɗanda aka ci zarafin su haƙƙinsu dama hukunta dukkan masu hannu a cikin lamarin.
PRNigeria Hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp