Home Labarai WAI na shirin kai gwamnatin Nijeriya kara gaban kotun ECOWAS

WAI na shirin kai gwamnatin Nijeriya kara gaban kotun ECOWAS

Ƙungiyar kare haƙƙin dan Adam, yaƙi da rashin adalci dama bibiya akan shugabanci nagari wato War Against Injustice (WAI), ta bayyana shirinta na maka Gwamnatin Najeriya a Kotun ECOWAS nan bada jimawa ba.
Babban Daraktan ƙungiyar Kwamared Umar Ibrahim Umar ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da ya aiko wa manema labarai a Lahadi, biyo bayan Jawabin da Shugaban ƙasar Bola Tinubu yayi wanda ya nuna rashin damuwa da halin da Talakawan ƙasar ke ciki.
A cewar sa “Dole mu ɗauki wannan mataki a sakamakon yadda Gwamnatin ta yi burus da buƙatun da Al’ummar ƙasar suka gabatar mata a wannan lokaci na zanga-zanga, harma Jami’an tsaro suke cin zarafin ‘yan ƙasar dama kashe su”.
Haka kuma ya buƙaci jami’an tsaro suyi gaggawar kama ‘yan Siyasar da suka ɗauki nauyin ɓata zanga-zangar, ta hanyar hayo ‘yan dabar da suka farwa dukiyar al’umma dama kayan Gwamnati.
Bugu da ƙari ƙungiyar ta yi Allah-wadai da cin zarafin ‘yan Jaridar da aka yi a lokacin zanga-zangar, suna tsaka da aikin su na hidimtawa al’umma dama ƙasar gaba-ɗaya.
A ƙarshe ƙungiyar ta yi fatan dukkan ɓangarorin da suke da alaƙa da matakin da suke shirin ɗauka zasu basu haɗin kan da ya kamata, domin nemowa waɗanda aka ci zarafin su haƙƙinsu dama hukunta dukkan masu hannu a cikin lamarin.
PRNigeria Hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp