Home Bincike Bincike: Shin da gaske ne masu zanga-zangar #EndBadGovernance sun kwashe kayan abinci...

Bincike: Shin da gaske ne masu zanga-zangar #EndBadGovernance sun kwashe kayan abinci da mahaifiyar Dangote ta ajje a store?

Wani bidiyo da aka yada a kafar sada zumunta ta facebook, ya yi ikirarin cewa mahaifiyar attajirin nahiyar Afirka, guda cikin manyan ‘yan kasuwa, Aliko Dangote, Hajiya Mariya Sanusi Dantata, ta yafewa fisatattun matasan da suka balle mata wurin ajiyar kayan abinci, a yayin da ake gudanar da zanga-zangar  #Endbadgovernance a jihar Kano.

Masu amfani da kafar da dama sun yada wallafar a shafin na facebook.

PRNigeria ta gudnar da bincike da wa su alamomi da sunan Nura Ado Faruwa, sakamakon ya nuna babu wata wallafa irin wannan.

Haka kuma, PRNigeria ta fahimci cewa an yi wallafar ne ta asali da wannan suna matsayin wanda ya fara wallafawa, daga bisani ya goge.

PRNigeria ta bincike kafar internet domin gano ko akwai sanarwa ta musamman da aka fitar domin bayyana yafiyar da aka yiwa matasan.

A wata ganawa da PRNigeria ta yi da guda cikin ma’aikatan hajiya Mariya Sanusi ya tabbatar da cewa da gaske ne masu zanga-zanga sun kwashi kaya a wurin ajiyar kayan nata.

“An kwashi kayan abinci da suka hadar da shinkafa, siga, fulawa a wurin ajiyar dake unguwar koki a jihar Kano a ranar farko ta gudanar da zanga-zangar ta ‘EndBadGovernance’ gudana cikin masu taimaka mata da ya bukaci a sakaye sunansa a lokacin da yake ganawa da PRNigeria.

Ya kara da cewa mahaifiyar ta Dangote yanzu haka tana Makka tana gudanar da ibadar Umra, amma bata san da aukuwar lamarin ba.

“Bata ma san an balle mata wurin ajiyar kaya an kwashe kayan ba. Don haka batun cewa ta yafewa wadanda suka dauki kayan ma bata taso ba karya ce kawai.

Kammalawa: saboda wannan bayanin, PRNigeria ta yanke hukuncin cewa da gaske ne an balle wurin ajiyar kayan abinci na Mahaifiyar Dangote a yayin gudanar da zanga-zangar #EndBadGovernance da aka gudanar a fadin kasa, a yayin da ita kuma tana kasar Saudi Arabia tana gudanar da ibadar Umra. Amma labarin da ake yadawa cewa ta yafewa wadanda suka balle wurin ajiyar karya ce kawai daga yau 4 ga watana Agustan 2024

 

PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp