Home Labarai WAI na shirin kai gwamnatin Nijeriya kara gaban kotun ECOWAS

WAI na shirin kai gwamnatin Nijeriya kara gaban kotun ECOWAS

Ƙungiyar kare haƙƙin dan Adam, yaƙi da rashin adalci dama bibiya akan shugabanci nagari wato War Against Injustice (WAI), ta bayyana shirinta na maka Gwamnatin Najeriya a Kotun ECOWAS nan bada jimawa ba.
Babban Daraktan ƙungiyar Kwamared Umar Ibrahim Umar ne ya sanar da hakan ta cikin wata sanarwa da ya aiko wa manema labarai a Lahadi, biyo bayan Jawabin da Shugaban ƙasar Bola Tinubu yayi wanda ya nuna rashin damuwa da halin da Talakawan ƙasar ke ciki.
A cewar sa “Dole mu ɗauki wannan mataki a sakamakon yadda Gwamnatin ta yi burus da buƙatun da Al’ummar ƙasar suka gabatar mata a wannan lokaci na zanga-zanga, harma Jami’an tsaro suke cin zarafin ‘yan ƙasar dama kashe su”.
Haka kuma ya buƙaci jami’an tsaro suyi gaggawar kama ‘yan Siyasar da suka ɗauki nauyin ɓata zanga-zangar, ta hanyar hayo ‘yan dabar da suka farwa dukiyar al’umma dama kayan Gwamnati.
Bugu da ƙari ƙungiyar ta yi Allah-wadai da cin zarafin ‘yan Jaridar da aka yi a lokacin zanga-zangar, suna tsaka da aikin su na hidimtawa al’umma dama ƙasar gaba-ɗaya.
A ƙarshe ƙungiyar ta yi fatan dukkan ɓangarorin da suke da alaƙa da matakin da suke shirin ɗauka zasu basu haɗin kan da ya kamata, domin nemowa waɗanda aka ci zarafin su haƙƙinsu dama hukunta dukkan masu hannu a cikin lamarin.
PRNigeria Hausa
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp