Home Bincike Bincike: Shin da gaske ne masu zanga-zangar #EndBadGovernance sun kai hari kasuwar...

Bincike: Shin da gaske ne masu zanga-zangar #EndBadGovernance sun kai hari kasuwar hausawa dake jihar Imo?

Akwai wani bidiyo maras kyan gani da ya yake yawo a kafafen sada zumunta na zamani dake ikirarin cewa al’ummar hausawa, da ya hadar da kasuwarsu da ake kira da Avu market aka tarwatsa a yayin zanga-zangar #EndBadGovernance.

Wani bidiyo dauke da wata murya cikin harshen hausa wadda ke ikirarin masu zanga-zanga sun kone dukkan unguwannin da hausawa suke an kone su kurmus a jihar Imo.

Mai Magana na cewa al’ummar hausawa da jagororinsu suka yi watsi da lamurransu, ga halin da suke ciki, ya kuma bukaci dukkan wanda ya kalli bidiyon ya yada domin wani ya gani.

Domin tabbatar da sahihancin ikirarin PRNigeria ta bincike bidiyon a nutse, inda ta karkasa shi kashi-kashi, domin yin amfani da hanyar gano ingancin bidiyo na (reverse image search)

Sakamakon ya nuna man cewa an wallafa bidiyon a shafin facebook mai suna Nuru Shehu, shekara daya da ta gabata, a ranar 29 ga watan yunin 2023.

Wallafar a shafin facebook ta sami like dubu 9, inda mutane dubu 1 da dari 7 suka tofa albakacin bakinsu, mutane dubu 13 suka sake yada shi, sai mutane dubu dari 433 suka kalla.

A cigaba da bincike,  PRNigeria ta kira kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Imo ASP Okoye Henry, wanda ya tabbatar da cewa babu wata zanga-zanga da aka gudanar wadda ta kai ga tarwatsa kasuwancin hausawa.

ASP Okoye ya kara tabbatar da cewa bidiyon dake yawo aiki ne kawai na marasa son zaman lafiya, wanda kullum bukatarsu shi ne yadda wani bangarorin kasar zasu kasance cikin tashin hankali da juna.

Ya bayyana cewa bidiyon dake yawo na wata gobarace da ta kama a kasuwar ta Avu, a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

KAMMALAWA: bisa binciken da PRNigeria ta gudanar ikirarin cewa an kone wurin zaman ‘yan Arewa da kasuwarsu a jihar Imo a lokacin zanga-zanga ba gaskiya bane labara ne na raba kawunan Al’umma.

By PRNigeria

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp