Home Labarai An kama telan dake dinka Tutar Rasha ga masu Zanga-Zanga a Kano

An kama telan dake dinka Tutar Rasha ga masu Zanga-Zanga a Kano

Rundunar ‘yan sandan Nijeriya, ta sanar da kama wani Ahmed Tela, wanda take zargi da dinka tutocin kasar Rasha da wasu masu zanga-zanga ke amfani da su a lokacin zanga-zanga a Kano da wasu jihohin Arewa.

An kuma kama masu zanga-zanga kimanin 30 da ke dauke da tutocin tare da tsare su.

Kakakin rundunar ‘yan sandan Najeriya Olumuyiwa Adejobi ne ya bayyana hakan ga manema labarai a hedikwatar hukumar ta farin kaya (DSS) a wani taron manema labarai da ofishin mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro ya shirya.

An hangi yadda wasu masu zanga-zangar ke fitowa kan manyan titunan Nijeriya musamman jihohin Kano, Kaduna, Bauchi da wasu jihohin Arewacin Nijeriya dauke da tutocin kasar Rasha musamman a wannan rana ta 5 da fara Zanga-zangar adawa da tsadar rayuwa a kasar.

An ga masu zanga-zangar dauke da tutocin kasar Rasha suna zagaya tituna suna rera wakoki daban-daban tare da wasu dauke da alluna.

Adejobi ya ce daga tutocin wasu kasashe a Najeriya, wadda aka kasa ce mai cin gashin kanta, laifi ne, inda ya kara da cewa wadanda aka kama da wadanda suka dauki nauyinsu za a tuhume su kamar yadda dokar kasar ta tanada kan laifukan da suka aikata.

“Da safiyar yau ne muka kama wani ‘Ahmed Tela’ daga karamar hukumar Nasarawa a jihar Kano, bisa laifin samar da tutocin kasar Rasha masu yawan gaske da ake baiwa matasan Najeriya domin su dagawa.

“Mun kama shi, Kuma muna kara farautar wasu musamman wadanda suka sa ka su. Kamar yadda nake magana da ku, haka abin ya faru a Kaduna. mun sami damar kama 30 daga cikinsu dauke da tutocin Rasha ” in ji babban jami’in ‘yan sandan.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp