Home Labarai Rasha ta Magantu kan Zanga-zangar Nijeriya

Rasha ta Magantu kan Zanga-zangar Nijeriya

Gwamnatin Rasha ta nesanta kanta da wasu masu zanga-zanga a Najeriya waɗanda aka gani suna ɗaga tutar ƙasar Rasha.

A ranar Litinin an ga tuɗaɗowar ɗumbin masu zanga -zanga a jihohin arewacin Najeriya kamar Zamfara da Kaduna, inda wasu daga cikinsu ke ɗaga tutar Rasha.

Sai dai a wata sanarwa da aka sanya a shafin na intanet, ofishin jakadancin Rasha a Najeriya ya ce matakin da wasu masu zanga-zanga suka ɗauka na amfani da tutar Rasha mataki ne na ƙashin kansu, kuma wannan ba shi ne ainahin manufa da muradin ƙasar Rasha ba.

Sanarwar ta ce: “Kamar a kodayaushe, muna sake jaddada cewa Rasha ba ta shiga cikin harkokin cikin gida na ƙasashe masu ƴanci, ciki kuwa har da Najeriya.”

Rasha ta ce tana martaba mulkin dimokuraɗiyyar Najeriya kuma tana kyautata zaton cewa zanga-zangar da ake yi a ƙasar na kan doka da kuma tsari na mulkin demokuraɗiyya.

Sanarwar ta kammala da cewa “sai dai za mu yi Allah-wadai idan wannan zanga-zanga ta rikiɗe zuwa tarzoma.”

Dubban masu zanga-zanga ne suka hau kan titunan biranen Najeriya a zanga-zangar adawa da matsin rayuwa da al’ummar ƙasar ke ciki.

Zanga-zangar ta ci gaba a ranar Litinin bayan da ƙungiyoyin da ke jagorantarta suka ce jawabin da shugaban ƙasar ya yi a ranar Lahadi bai taɓo buƙatunsu ba.

An tsara gudanar da zanga-zangar ne tsawon kwana goma, daga 1 zuwa 10 ga watan Agustan 2024.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp