Home Labarai Masu zanga-zanga sun bukaci Tinubu ya kori IG

Masu zanga-zanga sun bukaci Tinubu ya kori IG

Masu shirya zanga-zangar tsadar rayuwa a Nijeriya sun bukaci shugaban kasa Bola Tinubu daya gaggauta cire babban Sifetan ‘yan sandan kasar Olukayode Egbetokun, bisa zargin kisan masu zanga zanga tsadar rayuwa ta ”Endbadgovernance”.

Wannan dai na kunshe ta cikin wata sanarwa da kodinetan kungiyar ”take it back movement” Sanyaolu Juwon ya fitar, inda ta zargi jami’an ‘yan sanda kasar nan da hallaka masu zanga-zanga akalla 40 a lokacin da ake gudanar da ita kasar.

Haka kuma kungiyar tace jami’an sun tsare akalla mutane dubu 1 dake zanga-zanga kan tsadar rayuwa a wasu jihohin kasar nan. Don haka ya zama wajibi shugaban kasa ya kori babban sifeton ‘yan sandan bisa alhakin hallaka mutuane 40 wadanda aka harbe da alburushi a kokarin su na inganta laumar da zasu kai baka.

Kawo yanzu dai mutane dubu daya rundnar ‘yan sandan kasar na ke tsare da su, inda dakarun ke tsare da mutane 632 a jihar kano inda suka kama mutane 109 a jihar sokoto a gidajen ajiya da gyaran hali.

Ko da yake daai a iya cewa zanga-zangar ta dauki wani salo musamman a wasu jihohin arewacin kasar inda a safiyar wannan rana ake gudanar da salloli da addu’oin alkunutu, domin magance tsadar rayuwa a fadin kasar.

 

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp