Home DUNIYA Hadarin Jirgi ya hallaka mutane 62 a Brazil

Hadarin Jirgi ya hallaka mutane 62 a Brazil

Wani haɗarin ƙaramin jirgin sama a Brazil, yayi sanadin mutuwar mutane 62 da ke cikin jirgin.

Jami’ai a ƙasar sun ce babu ko da mutum guda da ya rayu a haɗarin da ya afku a birnin Sao Paulo.

Kamfanin jirgin saman da ya faɗi wato Voepass ya tabbatar da faruwar lamarin cikin daren jiya.

Mahukuntan a ƙauyen Valinhos da jirgin ya faɗi, sun ce iya mutanen da ke cikin jirgin haɗarin ya shafa, amma kuma ya lalata gidaje da sauran gine-ginen da ya faɗa kansu.

A nasa ɓangaren shugaban ƙasar ta Brazil Luiz Inacio Lula da Silva ya jajantawa al’ummar ƙasar kan faruwar lamarin, yana mai cewa sam bai ji dadin yadda zai sanar da faruwar baƙin labarin ba amma ya zama dole ƴan ƙasar su san cewa ƴan uwan su fasinjojin jirgin 58 da kuma ma’aikata biyu sun mutu.

Har yanzu dai babu cikakken bayani kan dalilin faɗuwar jirgin daga hukumar kula da sufurin jiragen sama ta ƙasar, sai dai kuma faya-fayan bidiyo sun nuna yadda wasu sassan jirgin suka kama da wuta tun yana sama kafin daga bisani ya rikito.

Bayanai sun ce jirgin ƙirar Flightradar 24 wanda aka samar a shekaar 2010 na da matuƙar ƙarfi da kuma juriya wajen aiki, kuma an samar da shi ne a jihar Parana ta ƙasar.

sao dao Gwamnatin kasar ta ayyana zaman makoki kasar, inda shugaban kasar lula De silva ya bukaci yin shiru na wani lokaci.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp