Home Labarai Masu zanga-zanga sun bukaci Tinubu ya kori IG

Masu zanga-zanga sun bukaci Tinubu ya kori IG

Masu shirya zanga-zangar tsadar rayuwa a Nijeriya sun bukaci shugaban kasa Bola Tinubu daya gaggauta cire babban Sifetan ‘yan sandan kasar Olukayode Egbetokun, bisa zargin kisan masu zanga zanga tsadar rayuwa ta ”Endbadgovernance”.

Wannan dai na kunshe ta cikin wata sanarwa da kodinetan kungiyar ”take it back movement” Sanyaolu Juwon ya fitar, inda ta zargi jami’an ‘yan sanda kasar nan da hallaka masu zanga-zanga akalla 40 a lokacin da ake gudanar da ita kasar.

Haka kuma kungiyar tace jami’an sun tsare akalla mutane dubu 1 dake zanga-zanga kan tsadar rayuwa a wasu jihohin kasar nan. Don haka ya zama wajibi shugaban kasa ya kori babban sifeton ‘yan sandan bisa alhakin hallaka mutuane 40 wadanda aka harbe da alburushi a kokarin su na inganta laumar da zasu kai baka.

Kawo yanzu dai mutane dubu daya rundnar ‘yan sandan kasar na ke tsare da su, inda dakarun ke tsare da mutane 632 a jihar kano inda suka kama mutane 109 a jihar sokoto a gidajen ajiya da gyaran hali.

Ko da yake daai a iya cewa zanga-zangar ta dauki wani salo musamman a wasu jihohin arewacin kasar inda a safiyar wannan rana ake gudanar da salloli da addu’oin alkunutu, domin magance tsadar rayuwa a fadin kasar.

 

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp