Home Labarai Masu zanga-zanga sun bukaci Tinubu ya kori IG

Masu zanga-zanga sun bukaci Tinubu ya kori IG

Masu shirya zanga-zangar tsadar rayuwa a Nijeriya sun bukaci shugaban kasa Bola Tinubu daya gaggauta cire babban Sifetan ‘yan sandan kasar Olukayode Egbetokun, bisa zargin kisan masu zanga zanga tsadar rayuwa ta ”Endbadgovernance”.

Wannan dai na kunshe ta cikin wata sanarwa da kodinetan kungiyar ”take it back movement” Sanyaolu Juwon ya fitar, inda ta zargi jami’an ‘yan sanda kasar nan da hallaka masu zanga-zanga akalla 40 a lokacin da ake gudanar da ita kasar.

Haka kuma kungiyar tace jami’an sun tsare akalla mutane dubu 1 dake zanga-zanga kan tsadar rayuwa a wasu jihohin kasar nan. Don haka ya zama wajibi shugaban kasa ya kori babban sifeton ‘yan sandan bisa alhakin hallaka mutuane 40 wadanda aka harbe da alburushi a kokarin su na inganta laumar da zasu kai baka.

Kawo yanzu dai mutane dubu daya rundnar ‘yan sandan kasar na ke tsare da su, inda dakarun ke tsare da mutane 632 a jihar kano inda suka kama mutane 109 a jihar sokoto a gidajen ajiya da gyaran hali.

Ko da yake daai a iya cewa zanga-zangar ta dauki wani salo musamman a wasu jihohin arewacin kasar inda a safiyar wannan rana ake gudanar da salloli da addu’oin alkunutu, domin magance tsadar rayuwa a fadin kasar.

 

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp