Home Labarai Masu zanga-zanga sun bukaci Tinubu ya kori IG

Masu zanga-zanga sun bukaci Tinubu ya kori IG

Masu shirya zanga-zangar tsadar rayuwa a Nijeriya sun bukaci shugaban kasa Bola Tinubu daya gaggauta cire babban Sifetan ‘yan sandan kasar Olukayode Egbetokun, bisa zargin kisan masu zanga zanga tsadar rayuwa ta ”Endbadgovernance”.

Wannan dai na kunshe ta cikin wata sanarwa da kodinetan kungiyar ”take it back movement” Sanyaolu Juwon ya fitar, inda ta zargi jami’an ‘yan sanda kasar nan da hallaka masu zanga-zanga akalla 40 a lokacin da ake gudanar da ita kasar.

Haka kuma kungiyar tace jami’an sun tsare akalla mutane dubu 1 dake zanga-zanga kan tsadar rayuwa a wasu jihohin kasar nan. Don haka ya zama wajibi shugaban kasa ya kori babban sifeton ‘yan sandan bisa alhakin hallaka mutuane 40 wadanda aka harbe da alburushi a kokarin su na inganta laumar da zasu kai baka.

Kawo yanzu dai mutane dubu daya rundnar ‘yan sandan kasar na ke tsare da su, inda dakarun ke tsare da mutane 632 a jihar kano inda suka kama mutane 109 a jihar sokoto a gidajen ajiya da gyaran hali.

Ko da yake daai a iya cewa zanga-zangar ta dauki wani salo musamman a wasu jihohin arewacin kasar inda a safiyar wannan rana ake gudanar da salloli da addu’oin alkunutu, domin magance tsadar rayuwa a fadin kasar.

 

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp