Ba a ba mu umarnin fara biyan masu yi wa ƙasa hidima N70,000 ba – NYSC

Hukumar da ke Kula da Matasa Masu yi wa Kasa Hidima (NYSC) ta ce ba ta umarci matasa masu hidimar ƙasa su gyara asusun ajiyarsu na bankuna domin ta fara biyan su N70,000 ba.

NYSC dai a yanzu haka tana biyan matasan Naira 33,000 a kowanne wata a matsayin kuɗaɗen alawus-alawus.

Hukumar ta bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da Daraktanta na yaɗa labarai, Eddy Megwa, ya fitar ranar Lahadi a Abuja.

A cewar sanarwar, yanzu haka kururuwar na nan ta karaɗe shafukan sada zumunta na zamani, inda ta ce amma ƙarya ce tsagwaronta.

Eddy ya kuma ce, “Muna sanar da matasa masu yi wa ƙasa hidima, iyaye da sauran jama’a cewa har yanzu ba mu karɓi umarni daga sashen gwamnati da ke kuka da batun biyan albashi ba a kan lamarin.

“Saboda haka, ba zai yiwu NYSC mu bayar da wani umarni ba a kan lamarin.

“Matasa masu yi wa ƙasa hidima sun san hanyoyin da muke bi idan za mu fitar musu da sanarwa, don haka su yi watsi da wannan maganar.

“Daga wannan sanarwar, muna ba matasan shawara da su daina yarda masu neman tayar da zaune tsaye suna wasa da hankulansu,” in ji shi.

A ƙarshen watan da ya gabata ne dai Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya rattaba hannu a kan sabuwar dokar mafi ƙarancin albashi wanda yanzu ya koma Naira 70,000.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 4 hours 38 minutes 42 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 6 hours 20 minutes 7 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com