Home Labarai Ba a ba mu umarnin fara biyan masu yi wa ƙasa hidima...

Ba a ba mu umarnin fara biyan masu yi wa ƙasa hidima N70,000 ba – NYSC

Hukumar da ke Kula da Matasa Masu yi wa Kasa Hidima (NYSC) ta ce ba ta umarci matasa masu hidimar ƙasa su gyara asusun ajiyarsu na bankuna domin ta fara biyan su N70,000 ba.

NYSC dai a yanzu haka tana biyan matasan Naira 33,000 a kowanne wata a matsayin kuɗaɗen alawus-alawus.

Hukumar ta bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da Daraktanta na yaɗa labarai, Eddy Megwa, ya fitar ranar Lahadi a Abuja.

A cewar sanarwar, yanzu haka kururuwar na nan ta karaɗe shafukan sada zumunta na zamani, inda ta ce amma ƙarya ce tsagwaronta.

Eddy ya kuma ce, “Muna sanar da matasa masu yi wa ƙasa hidima, iyaye da sauran jama’a cewa har yanzu ba mu karɓi umarni daga sashen gwamnati da ke kuka da batun biyan albashi ba a kan lamarin.

“Saboda haka, ba zai yiwu NYSC mu bayar da wani umarni ba a kan lamarin.

“Matasa masu yi wa ƙasa hidima sun san hanyoyin da muke bi idan za mu fitar musu da sanarwa, don haka su yi watsi da wannan maganar.

“Daga wannan sanarwar, muna ba matasan shawara da su daina yarda masu neman tayar da zaune tsaye suna wasa da hankulansu,” in ji shi.

A ƙarshen watan da ya gabata ne dai Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya rattaba hannu a kan sabuwar dokar mafi ƙarancin albashi wanda yanzu ya koma Naira 70,000.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp