Home Labarai Gwamnatin Kano ta janye dokar hana fita gaba daya a jihar

Gwamnatin Kano ta janye dokar hana fita gaba daya a jihar

Gwamnan jihar Kano ya sanar da janye dokar hana fita da ya saka sakamakon tarzomar da ta biyo bayan zanga-zanga kan matsin rayuwa a Nijeriya.

Abba Kabir Yusuf ya sanar da matakin ne yayin da yake yi wa ‘yanjarida jawabi a jihar yau Litinin bayan wata ziyarara gani da ido da ya kai harabar kotun da matasa suka yi barna a ranar zanga-zangar.

“Gwamnati ta janye wannan doka gaba ɗaya, kuma mai girma gwamna ya jinjina wa malamai da jami’an tsaro da suka jajirce don ganin an samu zaman lafiya,” kamar yadda Kwamashinan Yaɗa Labarai Baba Halilu Dantiye ya shaida wa manema labarai cikin wani saƙon murya.

Gwamnati ta saka dokar a ranar 1 ga watan Agusta bayan wasu ɓata-gari sun auka wa gine-gine da shagunan mutane tare da yin wawashe kayayyaki a ranar farko ta zanga-zangar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp