Gwamnatin Kano ta janye dokar hana fita gaba daya a jihar

Gwamnan jihar Kano ya sanar da janye dokar hana fita da ya saka sakamakon tarzomar da ta biyo bayan zanga-zanga kan matsin rayuwa a Nijeriya.

Abba Kabir Yusuf ya sanar da matakin ne yayin da yake yi wa ‘yanjarida jawabi a jihar yau Litinin bayan wata ziyarara gani da ido da ya kai harabar kotun da matasa suka yi barna a ranar zanga-zangar.

“Gwamnati ta janye wannan doka gaba ɗaya, kuma mai girma gwamna ya jinjina wa malamai da jami’an tsaro da suka jajirce don ganin an samu zaman lafiya,” kamar yadda Kwamashinan Yaɗa Labarai Baba Halilu Dantiye ya shaida wa manema labarai cikin wani saƙon murya.

Gwamnati ta saka dokar a ranar 1 ga watan Agusta bayan wasu ɓata-gari sun auka wa gine-gine da shagunan mutane tare da yin wawashe kayayyaki a ranar farko ta zanga-zangar.

PRNigeria Hausa

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 11 hours 58 minutes 58 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 13 hours 40 minutes 23 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com