Home Labarai Dangote ya musanta kayyade farashin Man fetur

Dangote ya musanta kayyade farashin Man fetur

Shugabannin matatar man Ɗangote sun yi watsi da rahotannin da ke cewa an ƙayyade farashin man fetur a kan naira 600 kan kowacce lita, inda ta bayyana rahotannin a matsayin jita-jita marar tushe.

A wata sanarwa da babban jami’in kula da harkokin kasuwanci da sadarwa na rukunin kamfanonin Dangote, Anthony Chiejina, ya fitar a shafin sada zumunta na X, ya yi tsokaci kan jita-jitar da ake ta yaɗawa da ke cewa matatar na tattaunawa da ƙungiyar dillalan man fetur ta ƙasar IPMAN, a kan yadda za a cimma matsaya wajen sayar da man a kan naira 600 kan kowacce lita.

Kamfanin ya fayyace cewa bai ƙulla wata yarjejeniya da ƙungiyar ta IPMAN ba, ya kuma jaddada cewa duk wani mataki da kamfaninsu ko matatar za ta ɗauka za a sanar a hukumance.

Sanarwar ta cewa “An jawo hankalinmu kan labarin da ke cewa kamfanin Dangote ya ƙayyade farashin man fetur kan naira 600 kan kowace lita, a jiya Talata, 13 ga watan Agustan 2024.”

“Za mu so mu fayyace cewa ba mu da wata alaƙar kasuwanci da IPMAN a yanzu.”

Ya ce “Ba mu taɓa tattaunawa kan farashin man fetur da IPMAN ba kuma ba su da wani hurumin yin magana a madadinmu.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp