Home Labarai Farashin kayan abinci ya sauka a Nijeriya

Farashin kayan abinci ya sauka a Nijeriya

Hukumar ƙididdiga ta Najeriya ta sanar a ranar Alhamis cewa, farashin kaya a ƙasar ya sauka a karon farko da kashi 33.4 cikin 100 a watan Yuli inda aka kwatanta da kashi 34.19 cikin 100 a watan Yunin shekarar da muke ciki.

Kayayyakin da farashin nasu ya sauka sun haɗa da shinkafa da masara da ƙwai da burodi da man fetur.

To sai dai kuma farashin makamashi na ci gaba da hauhawa a cikin shekara ɗaya da ta wuce a cewar hukumar.

Najeriya dai ta fara aiwatar da manufofin farfaɗo da tattalin arzikin ƙasar tun a bara.

Ƙasar ta dauki matakai kamar cire tallafin man fetur da kuma farfaɗo da darajar kuɗin ƙasar, naira.

Shugaba ƙasar Bola Tinubu ya ce sauye-sauyen na da matukar muhimmanci kuma ya zama dole da nufin farfaɗo da tattalin arziƙin.

A farkon watan Augusta ne ƴan kasar suka gudanar da zanga-zanga a kan matsin rayuwa ta kwana 10 don matsawa gwamnati ɗaukar matakan sassauta al’amura.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp