Tinubu ya rantsar da sabuwar Babbar mai Shari’a ta Najeriya

Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya rantsar da Mai shari’a Kudirat Kekere-Ekun a matsayin mai riƙon muƙamin Babbar mai Shari’a ta Najeriya, kafin Majalisar Dattijan ƙasar ta tabbatar da naɗin nata.

Shugaban ya rantsar da ita ne a ranar Juma’a bayan dawowarsa daga Faransa.

Mai shari’a Kekere-Ekun za ta maye gurbin Mai shari’a Olukayode Ariwoola, wanda ya yi ritaya bayan ya kai shekara 70 a duniya.

A ƙa’idar Kotun Ƙolin, babban alƙali mai biye da shi ne zai maye gurbinsa, wanda hakan ya sa Mai shari’a Kudirat ce za ta maye gurbin da zai bari.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com