Home Labarai Ƴansanda sun tabbatar da ceto ɗaliban likitanci 20 da aka sace a...

Ƴansanda sun tabbatar da ceto ɗaliban likitanci 20 da aka sace a jihar Benue

Rundunar ƴansandan Najeriya ta tabbatar da sakin ɗaliban nan 20 da ke karatun aikin likita, waɗanda aka sace a jihar Benue a ranar Juma’a ta makon da ya gabata.

A wata sanarwa da kakakin ƴansandan ƙasar, Muyiwa Adejobi, ya fitar ya ce a jiya Juma’a ne ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, ya ceto ɗaliban da aka riƙe su a dajin Ntunkon, da ke ƙaramar hukumar ADO ta jihar Benue, ba tare da an biya wani kuɗi ba.

Tashar talabijin ta Channels, ta ce wata majiya da ta tabbatar da ingancinta, ta tabbatar mata cewa an yi amfani da wasu jiragen yaƙi masu sauƙar ungulu guda uku a aikin ceto ɗaliban, inda ta ce an kama wasu daga cikin masu garkuwar wasu kuma an kashe su.

A ranar Alhamis ta makon da ya gabata ne aka sace ɗaliban na jami’ar Maiduguri da jami’ar Jos tare da likitocin da suke tare da su a kan hanyarsu ta zuwa wani taro.

Ƴan kwanaki kaɗan bayan sace su, ƴan bindigar sun tuntuɓi iyalan ɗaliban suna son a ba su kuɗin fansa naira miliyan 50, kafin su sake su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Ƴan Bindiga sun Buƙaci Kudin Fansa Kafin Sako Dattijan da Suka je Sulhu a ZamfaraMayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSF
X whatsapp