Home Labarai Ƴansanda sun tabbatar da ceto ɗaliban likitanci 20 da aka sace a...

Ƴansanda sun tabbatar da ceto ɗaliban likitanci 20 da aka sace a jihar Benue

Rundunar ƴansandan Najeriya ta tabbatar da sakin ɗaliban nan 20 da ke karatun aikin likita, waɗanda aka sace a jihar Benue a ranar Juma’a ta makon da ya gabata.

A wata sanarwa da kakakin ƴansandan ƙasar, Muyiwa Adejobi, ya fitar ya ce a jiya Juma’a ne ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, ya ceto ɗaliban da aka riƙe su a dajin Ntunkon, da ke ƙaramar hukumar ADO ta jihar Benue, ba tare da an biya wani kuɗi ba.

Tashar talabijin ta Channels, ta ce wata majiya da ta tabbatar da ingancinta, ta tabbatar mata cewa an yi amfani da wasu jiragen yaƙi masu sauƙar ungulu guda uku a aikin ceto ɗaliban, inda ta ce an kama wasu daga cikin masu garkuwar wasu kuma an kashe su.

A ranar Alhamis ta makon da ya gabata ne aka sace ɗaliban na jami’ar Maiduguri da jami’ar Jos tare da likitocin da suke tare da su a kan hanyarsu ta zuwa wani taro.

Ƴan kwanaki kaɗan bayan sace su, ƴan bindigar sun tuntuɓi iyalan ɗaliban suna son a ba su kuɗin fansa naira miliyan 50, kafin su sake su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Rahoton ‘Yan Sanda ya Danganta Kashi 70% na Laifuka a Kano da Shaye-Shayen Miyagun Ƙwayoyi, Ya Gano Mutane 513 da ake Zargin Masu Safara NePantami Ya Samu Karfin Gwiwa Yayin Da Jama'a Ke Taya Shi Murna a Lokacin Ziyarar Ayyuka a GombeMa’aikatar Tsaro ta yi Karin Bayani Kan Yarjejeniyar Yaki da Ta’addanci da Turkiyya, ta Karyata Zargin ‘Jihadi’Tinubu na Neman Amincewar Majalisar Dattawa kan Sabon Rancen $516.3mGadon Mulkin Gombe: Wa Ke Jin Tsoron Tasirin Pantami Daga Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Masu Kera Makamai ba Bisa Ka'ida ba a Filato, Sun Kama Wadanda ake Zargi da Ta'addanci a NijarShin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa Malami
X whatsapp