Home General Gwamnatin Nijeriya ta amince a kori ma’aikata masu takardar karatu ta bogi...

Gwamnatin Nijeriya ta amince a kori ma’aikata masu takardar karatu ta bogi daga ƙasar Benin da Togo

Gwamnatin Najeriya ta bayar da amince a kori duk ma’aikata na gwamnati da waɗanda ba na gwamnati ba, waɗanda suke da takardar shedar karatu ta bogi, da suka samu daga Jamhuriyar Benin da Togo,

Ministan Ilimi Farfesa Tahir Mamman shi ne ya bayyana haka a, yayin wani taron manema labarai, jiya Juma’a a Abuja, lokacin da yake bayyana irin nasarorin da ya ce ya samu a tsawon shekara ɗaya a ma’aikata.

Mamman ya ce an amince da matakin ne a lokacin taron majalisar zartarwa ta ƙasar kwanan nan.

Ministan ya bayyana cewa ƴan ƙasar sama da 22,500 ne ke ɗauke da takardar shedar karatu ta bogi da suka samu daga ƙasashe irin su, Jamhuriyar Benin da Togo, a tsakanin 2019 da 2023.

Ya ce sama da ɗalibai 21, 600, suka samu takardun shedar karatun daga jami’o’in da ba a tabbatar da ingancinsu ba a Jamhuriyar Benin yayin da 1,105 su ma suka samu irin waɗannan takardu daga jami’o’in da ba a tabbatar da ingancin nasu ba a Togo.

Ya ƙara da cewa a don haka ne gwamnati ta kafa wani kwamiti na musamman na haɗin gwiwa tsakanin ma’aikatu domin gudanar da bincike kan takardun shedae karatun, cibiyoyin da ke wannan cuwa-cuwa a ciki da wajen Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp