Home General Gwamnatin Nijeriya ta amince a kori ma’aikata masu takardar karatu ta bogi...

Gwamnatin Nijeriya ta amince a kori ma’aikata masu takardar karatu ta bogi daga ƙasar Benin da Togo

Gwamnatin Najeriya ta bayar da amince a kori duk ma’aikata na gwamnati da waɗanda ba na gwamnati ba, waɗanda suke da takardar shedar karatu ta bogi, da suka samu daga Jamhuriyar Benin da Togo,

Ministan Ilimi Farfesa Tahir Mamman shi ne ya bayyana haka a, yayin wani taron manema labarai, jiya Juma’a a Abuja, lokacin da yake bayyana irin nasarorin da ya ce ya samu a tsawon shekara ɗaya a ma’aikata.

Mamman ya ce an amince da matakin ne a lokacin taron majalisar zartarwa ta ƙasar kwanan nan.

Ministan ya bayyana cewa ƴan ƙasar sama da 22,500 ne ke ɗauke da takardar shedar karatu ta bogi da suka samu daga ƙasashe irin su, Jamhuriyar Benin da Togo, a tsakanin 2019 da 2023.

Ya ce sama da ɗalibai 21, 600, suka samu takardun shedar karatun daga jami’o’in da ba a tabbatar da ingancinsu ba a Jamhuriyar Benin yayin da 1,105 su ma suka samu irin waɗannan takardu daga jami’o’in da ba a tabbatar da ingancin nasu ba a Togo.

Ya ƙara da cewa a don haka ne gwamnati ta kafa wani kwamiti na musamman na haɗin gwiwa tsakanin ma’aikatu domin gudanar da bincike kan takardun shedae karatun, cibiyoyin da ke wannan cuwa-cuwa a ciki da wajen Najeriya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Rahoton ‘Yan Sanda ya Danganta Kashi 70% na Laifuka a Kano da Shaye-Shayen Miyagun Ƙwayoyi, Ya Gano Mutane 513 da ake Zargin Masu Safara NePantami Ya Samu Karfin Gwiwa Yayin Da Jama'a Ke Taya Shi Murna a Lokacin Ziyarar Ayyuka a GombeMa’aikatar Tsaro ta yi Karin Bayani Kan Yarjejeniyar Yaki da Ta’addanci da Turkiyya, ta Karyata Zargin ‘Jihadi’Tinubu na Neman Amincewar Majalisar Dattawa kan Sabon Rancen $516.3mGadon Mulkin Gombe: Wa Ke Jin Tsoron Tasirin Pantami Daga Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Masu Kera Makamai ba Bisa Ka'ida ba a Filato, Sun Kama Wadanda ake Zargi da Ta'addanci a NijarShin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa Malami
X whatsapp