Home General Mutane 3 sun mutu a rikicin ‘yan Shi’a da ‘yan sanda a...

Mutane 3 sun mutu a rikicin ‘yan Shi’a da ‘yan sanda a Abuja

An kashe ‘yansanda biyu da jikkata wasu biyu, sannan kuma wani ɗan kasuwa ya rasu bayan da aka harbe shi a wani rikici da ya tashi tsakanin da ‘yan Shi’a na ƙungiyar Harka Islamiyya a Najeriya, (IMN), mabiya Sheik Ibrahim El-Zakzaky, a kasuwar Wuse da ke Abuja.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa mutumin da aka harbe mai suna Amiru, an harbe shi a ƙirji ne lokacin da ‘yansanda suke rarakar masu zanga-zangar na Shi’a.

Jaridar ta ce wani da y ga abin da ya faru wanda ya nemi da kada a fadi sunansa ya ce an garzaya da mutumin asibitin Wuce Zone 3 inda a can ya ga ‘yansanda da dama da aka jikkata a rikicin, a don haka aka nufi asibitin Maitama da shi inda a kan hanya ya cika.

Mabiya kungiyar ta IMN dai na zanga-zangar da suke yi wa lakabi da Arbaeen, wato cika kwana arba’in bayan taron Ashura.

A wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar ‘yansandan babban birnin SP Josephine Adeh, ta fitar, ta tabbatar da kisan jami’ansu guda biyu da jikkata wasu biyu tare kuma da kona motocin ‘yansanda na sintiri uku a rikicin wanda ta ce ba gaira ba dalili mabiya kungiyar suka kai wa jami’ansu hari.

A sanarwar da ‘yansandan suka fitar sun ce, ”mabiya haramtacciyar kungiyar sun kai wa wajen binciken ababan hawa na ‘yansanda hari haka kawai, dauke da adda da bama-bamai hadin gida wadanda aka yi da kananzir a cikin kwalba, da kuma wukake.

Rundunar ta ce an kama mutane da dama, inda kwamishinan ‘yansandan birnin na Abuja CP Benneth C. Igweh, ya ce za a gurfanar da su a gaban kotu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp