Home General Kungiyar IMN ta ce an kashe mata mutane a Abuja

Kungiyar IMN ta ce an kashe mata mutane a Abuja

Rundunar ‘yansandan Nijeriya ta ce ta kama mabiya mazhabar shi’a da dama, bayan kisan jami’anta biyu yayin wata arangama a Abuja, babban birnin kasar.

Lamarin ya faru ne, lokacin da ‘yan shi’ar ke tattakin yaumul arba’in, da suke gudanarwa kowacce shekara.

Mai magana da yawun rundunar ‘yansandan Najeriya a birnin Abuja, SP josephine Ade ta ce jamianta na tsaka da aikinsu a wani wurin bincike da ke kusa da kasuwar Wuse ‘yan kungiyar ta IMN suka far musu.

‘’Yaran mu su na aiki, sai ga shi sun fito, mata a gaba da yara, mazan na ta baya, kawai kafin a ankara mai yake faruwa su ka fara jifa da bam din da suka yi da kwalba’’

‘’Ba abinda mu ka yi musu, kawai suka fara kai wa jami’an mu hari, suka kashemu na ‘yansanda guda biyu tare da raunata wasu uku sannan sun kona motocci guda uku’’ in ji ta

Rundunar ‘yansanda Najeriya ta ce su na kan gudanar bincike akan abinda ya haifar da yamutsin :

‘’Mun kama wasu ‘yan shi’a a lokacin kuma muna kan bincike domin mu san abinda ya haifar da yamutsin. Ba bu wani da aka kashe daga bangaren ‘yan shi’ar’’ in ji ta

Sai dai daya daga cikin jagororin kungiyar ta IMN Malam Abdullahi Muhammad Musa ya ce ba haka abin ya wakana ba.

Ya ce tun ranar jamu’a suka fitar da sanarwar a kan cewa za su fito su yi tattaki kamar yadda suka saba duk shekara:

“Lafiya lau muka zo Wuse 2, mu na zuwa kasuwar Wuse ‘yansanda su ka bude ma na wuta, wasu su ka yi gaba da tattakin, har mu ka je Berger su ma ‘yansandan da ke Berger su ka harba ma na hayaki mai sa hawaye, sun harbi mutane da dama, a gaba na wani ya mutu’’

Ya yi ikirarin cewa ‘yan sandan sun harbi mutane da dama tare da musanta zargin cewa suna rike da makamai kuma sun tare wuri

“Ba mu taba tare wa kowa hanya ba , Su dai kawai sun bude ma na wuta , ba yau su ka saba kashe mana mutane ba’’ in ji shi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp