Home Labarai Ranar Hausa – Ko kun san wanda ya samar da bikin ranar...

Ranar Hausa – Ko kun san wanda ya samar da bikin ranar Hausa?

Karo na 10 kenan da ake gudanar da bikin ranar hausa ta duniya dukkan shekara, an shirya bikin ne domin kara fadada harshen a duniya da kuma kara samun kyakkyawar alaka tsakanin Hausawa da abokan zaman su.

A hannu guda akan yi amfani da ranar wajen kara tunatar da juna hanyoyin da ya kamata abi domin fidda A’I daga rogo, daga matsalolin dake addabar su kama daga tsaro, hadin kai da dai sauransu.

Albarkacin wannan rana PRNigeria ta tattaunawa da wanda ya fara kawo shawarar gudanar da bikin ranar hausa. Abdulbaki Jari, Dan Jarida ne dake Aiki da kafar yada labarai ta TRT Africa dake Turkiyya.

Inda yace an fara samar da wannan rana ne a shafin Twitter wanda yanzu ya koma X, da zummar dawo da hankalin al’umma wajen nemo bakin zaren matsalolin dake addabar su.

“Ranar hausa ta samo asali a shafin twitter wanda yanzu ya koma shafin X, mun fara wannan biki ne a ranar 26 ga watan Agustan 2015, a lokacin nazo da shawarar cewa ya kamata yadda muke da yawa mu ware wata rana da zamu rinka tattaunawa da harshen hausa domin tunatar da juna tasirin harshe  da kuma al’ada da kuma abu mafi muhimmaci wanda shine hadin kai.

Yace sun dauki wannan mataki ne kan yadda suka ga ana zuwa shafin sada zumunta ana fada ana tattauna wasu batutuwa da basu da muhimmanci, mai ma kon tattauna masu muhimmanci.

“Maimakon ya zama ana amfani da shafukan ana wayar da kai da zummar ganin cewa an nema maganin wadannan matsalolin musamman ta hanyar ankarar da shuwagabanni”

“Allah cikin ikon shi da aka yi wannan kira mutane sun amsa kiran inda wasu suka zo da shawarwari, wasu kuma suka zo da raha da sauransu ana kawo Karin Magana, wanda suma dai akwai hikima cikin Karin maganar, don kamar yadda muka sani ko wacce Karin Magana akwai hikima a ciki.

Taken bikin ranar hausan na bana dai shine, “tsintsiya madaurinki daya” hada kai domin inganta tattalin arziki da samar da zaman lafiya da tsaro.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp